Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai Afrika
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari Afrika
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe Afrika
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS Afrika
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe Afrika

‘Yan Ta’adda Sun Hallaka Sojoji Da Fararen Hula A Arewa Maso Gabashin Najeriya
Published: March 9, 2026 at 6:22 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

‘Yan ta’adda sun hallaka a kalla sojoji 12 da farar hula uku a wani hari da suka kai cikin dare a arewa maso gabashin Nigeria, a cewar majiyoyi daga sojoji da kuma mazauna wurin ranar Litinin.

Harin ya auku a garuruwan Kukawa da Dalwa a jihar Borno, da kuma Goniri a jihar Yobe kuma ya biyo bayan wani harin da aka kai kwanaki garin Ngoshe.

Kungiyar Boko Haram sun farwa Kukawa kafin wayewar garin ranar Litinin, suka durfafi sansanin soji dake wajen, inda aka shafe sa’o’i uku ana musayar wuta. Daga bya sojoji sun yi nasara, amma kwamandan rundunar da wasu sojoji biyar sun rasa rayukan su. Dan majalisa mai wakiltar Kukawa, Karta Ma’aji, ya tabbatar da aukuwar harin.

A Dalwa kuma ‘yan ta’addan sun kashe sojoji biyu da farar hula uku, sannan suka kona gidaje 250. A Goniri kuma da ke jihar Yobe, nan ma sun kai hari sansanin soji, inda suka hallaka sojoji hudu, suka kuma kone motocin wurin.

Afrika, Labarai, Najeriya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Kudin Man Fetur Ya Karu Da Kashi 10 Cikin 100
Next Post: Gwamnatin Kasar Guinea Ta Soke Wasu Jam’iyyun Siyasa

Karin Labarai Masu Alaka

Amurka Da Isra’ila Sunkai Hari Kan Iran Amurka
Babban Hafsan Tsaron Najeriya Ya Gargadi Jama’ar Arewa Maso Gabas Afrika
Shugaba Tinubu Zai Kara Karbo Bashin Dala Miliyan 516 Afrika
Bangladesh Tasamu Rangwamen Harajin Da Amurka Ta Kakaba Mata Labarai
Hawan Nasarawa A Jihar Kano Afrika
Hukumar Hasashen Kasuwanci Na Zargin Saida Bayanan Sirri Amurka

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Gwamnonin Arewa “Mun Amince Da Samar Da ‘Yan Sandan Jihohi” Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Kasar Belarus Zata Taffawa Jamhuriyar Nijar Afrika
  • ‘Yan Tawayen Houthi Sunkai Hari Isra’ila Afrika
  • Birtaniya Zata Fara Raba Rigakafin Allurar Cutar Sankara Kimiya
  • NLC Ta Yabawa Gwamnan Gombe Inuwa Yahaya Najeriya
  • Kasashen Thailand Da Cambodia Sun Amince Da Tsagaita Wuta Labarai
  • Ana Cigaba Da Tattaunawa Tsakanin Trump Da Zelensky Domin Tsagaita Wuta A Ukraine Labarai
  • Kotu A Kasar Faransa Ta Daure Lumbala Shekaru 30 Bisa Laifin Cin Zarafi Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.