Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro Labarai
  • Za A Cigaba Da Tattaunawa Domin Kawo Karshen Yakin Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Afirka Ta Kudu Ta Bayyana Yadda Aka Yaudari ‘Yan Kasar Ake Tilasta Musu Ayyukan Bauta
Published: December 23, 2025 at 8:34 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Rahotanni daga Afirka ta kudu suna kara bayyana yadda aka yaudari wasu ‘yan kasar suka tafi Rasha da sunan aikin tsaro ko makamancin haka, sai suka sami kansu a fagen daga a Ukraine, wani mahaifi Dubandlela yana cikin annashuwa da alfahiri lokacin da dansa dan shekaru 20 da haifuwa ya sanya hanu cikin watan Yulin bana, zai tafi Rasha inda za’a horas da jami’in tsaro da zai bada kariya ga masu hanu da shuni ko masu fada a ji.

Wata biyar bayan tafiyarsa, yanzu Dubandlela yana cike da takaici da zullumi, inda Dansa ya fada hanun mayaudara daga kungiyoyin sojojin haya, inda dansa da wasu akalla ‘yan kasar Afirka ta kudu 16 aka dauke su kuma aka tura fagen yaki a Ukraine.

Dubandlela yana aibunta kansa kan hali da dansa ya sami kansa a ciki, kuma Kakakin shugaban Afirka ta kudu Cyril Ramphosa, yace gwamnati tana “daukar batun da matukar muhimmanci.”

Yace kokarin kubutar da matasan yana da sarkakiya sosai, Kuma suna magana da dukkan sassan a yakin tsakanin Rasha da Ukraine, amma Vincent Magwenya yace sun fi bada karfi ne a magana da Rasha saboda an tura matasan ne ba shiri cikin rundunar mayakanta, Ya kara da cewa sun sami labari cewa matasan suna cikin hadari sosai a yankin Donbas.

Kamar yadda kamfanin dillancin labarai na Reuters ya fada, yaudarar da aka yi wa matasan ba zata rasa nasaba da zargin da aka yi wa ‘yar tsohon shugaban kasar Jacob Zuma, Lamari da ya tilasta mata yin murabus daga mjalaisar dokokin kasar.

Ma’aikatar harkokin wajen Rashar bata maida martani ba, da aka nemi jin ta bakinta a rubuce kan hanyoyin yaudarar matasan, da halinda suke ciki a halin yanzu

Afrika

Post navigation

Previous Post: Jami’an Tsaro: Babu Abun Tashin Hankali Kan Shawagin Jiragen Amurka
Next Post: Asusun IMF Zai Bawa Kasar Misra Lamunin Sama Da Dala Biliyan 2

Karin Labarai Masu Alaka

Gwamnatin Najeriya Tace A Maboyar ‘Yan Ta’adda Aka Kai Harin Jilli Afrika
‘Yan Sandan Najeriya Sunyi Nasarar Hallaka ‘Yan Ta’adda A Katsina Afrika
Babu Alamar Tsagaita Wuta A Yakin Gabas Ta Tsakiya Afrika
Shugaba Putin Ya Bukaci Kawo Karshen Yaki Da Iran Afrika
Amurka Da Jamhuriyar Dimokraɗiyya Kwango Sun Fara Wata Tattaunawa Afrika
Shugaba Trump Yace Zai Dakatar Da Kai Hari Cibiyar Makamashin Iran Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jami’yar ADC A Najeriya Ta Kori Nafiu Bala
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro
  • ‘Yan Sanda Sun Kama Mutane 33 Bisa Zargin Kai Hari A Jihar Kwara
  • Papa Roma Leo Yayi Gargadi Game Da Rushewar Dimokraɗiyya
  • Jiragen Ruwa Suna Biyayya Ga Dokar Hana Ketare Ruwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Mahaifiyar Nasiru El Rufai Ta Rasu Afrika
  • An Yanke Mishi Hukuncin Kisa Saboda Neman Kudin Aure Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Da Haɗin Guiwar Gwamnatin Jihar Zamfara Suna Shirin Kawo Karshen Matsalar Tsaro A Jihar Rumbun Hotuna
  • Nnamdi Kanu Zai Daukaka Kara Har Zuwa Kotun Koli Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Trump Da Bin Salman Da Wasu Kasashe Za Su Sa Hannu A Rikicin Sudan Labarai
  • Man Da Matatar Dangote Take Fitarwa Zuwa Kasashen Afirka Ya Karu Afrika
  • Tinubu Ya Buƙaci Gwamnoni Su Mutunta Hukuncin Kotun Ƙoli Kan ’Yancin Kuɗin ƙananan Hukumomi Labarai
  • Paparoma Leo: Zai Kai Ziyara Ƙasar Angola Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.