Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama Afrika
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara Afrika
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe Afrika
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro Afrika
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa Afrika

Afirka Ta Kudu Ta Bayyana Yadda Aka Yaudari ‘Yan Kasar Ake Tilasta Musu Ayyukan Bauta
Published: December 23, 2025 at 8:34 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Rahotanni daga Afirka ta kudu suna kara bayyana yadda aka yaudari wasu ‘yan kasar suka tafi Rasha da sunan aikin tsaro ko makamancin haka, sai suka sami kansu a fagen daga a Ukraine, wani mahaifi Dubandlela yana cikin annashuwa da alfahiri lokacin da dansa dan shekaru 20 da haifuwa ya sanya hanu cikin watan Yulin bana, zai tafi Rasha inda za’a horas da jami’in tsaro da zai bada kariya ga masu hanu da shuni ko masu fada a ji.

Wata biyar bayan tafiyarsa, yanzu Dubandlela yana cike da takaici da zullumi, inda Dansa ya fada hanun mayaudara daga kungiyoyin sojojin haya, inda dansa da wasu akalla ‘yan kasar Afirka ta kudu 16 aka dauke su kuma aka tura fagen yaki a Ukraine.

Dubandlela yana aibunta kansa kan hali da dansa ya sami kansa a ciki, kuma Kakakin shugaban Afirka ta kudu Cyril Ramphosa, yace gwamnati tana “daukar batun da matukar muhimmanci.”

Yace kokarin kubutar da matasan yana da sarkakiya sosai, Kuma suna magana da dukkan sassan a yakin tsakanin Rasha da Ukraine, amma Vincent Magwenya yace sun fi bada karfi ne a magana da Rasha saboda an tura matasan ne ba shiri cikin rundunar mayakanta, Ya kara da cewa sun sami labari cewa matasan suna cikin hadari sosai a yankin Donbas.

Kamar yadda kamfanin dillancin labarai na Reuters ya fada, yaudarar da aka yi wa matasan ba zata rasa nasaba da zargin da aka yi wa ‘yar tsohon shugaban kasar Jacob Zuma, Lamari da ya tilasta mata yin murabus daga mjalaisar dokokin kasar.

Ma’aikatar harkokin wajen Rashar bata maida martani ba, da aka nemi jin ta bakinta a rubuce kan hanyoyin yaudarar matasan, da halinda suke ciki a halin yanzu

Afrika

Post navigation

Previous Post: Jami’an Tsaro: Babu Abun Tashin Hankali Kan Shawagin Jiragen Amurka
Next Post: Asusun IMF Zai Bawa Kasar Misra Lamunin Sama Da Dala Biliyan 2

Karin Labarai Masu Alaka

MDD: Fiye Da Farar Hula Metan 200 Suka Mutu A Sudan Afrika
Gwamnan Gombe Ya Yaba Da Hikima Da Jagorancin Sarkin Gombe A Shekaru 12 Na Jagoranci Afrika
Ranar Lahadi Anyi Zaben Shugaban Kasa A Congo Afrika
APC Ta Bayyana Abba Yusuf A Matsayin Halastaccen Ɗan Takara Bayan Cika Sharudda Afrika
Yakin Iran Da Isra’ila Da Amurka Zai Shafi Kasashen Afirka – Masana Afrika
Amurka Zata Tantance Fararen Fata ‘Yan Afirka Ta Kudu Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Fiye Da Mutane 15 A Kasar Australiya Labarai
  • Amurka Ta Kai Hari Kan ‘Yan ISISI A Jihar Sakkwato Bisa Rokon Gwamnatin Najeriya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Al’ummomin da Ambaliyar Ruwan Mokwa a Jihar Nejan Najeriya ta sharewa gidaje sun Koka. Najeriya
  • Tsohon Gwamnan Jihar Kano Rabi’u Musa Kwankwaso Ya Fice Daga NNPP Afrika
  • Hukumar Tsaron Civil Defence A Gombe Ta Samar Da Jami’ai Don Tabbatar Da Tsaro A Bukukuwan Karshen Shekara Labarai
  • Ko Meye Gaskiyar Rade-Radin Zanga-Zanga A Jos Dake Jihar Filato Labarai
  • Amurka Zata Tantance Fararen Fata ‘Yan Afirka Ta Kudu Afrika
  • Kasar Aljeriya Ta Soke Yarjejeniyar Jirgin Sama Tsakaninta Da Daular Larabawa Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.