Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u Afrika
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa Afrika
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa Afrika
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed Afrika

Ranar Lahadi Anyi Zaben Shugaban Kasa A Congo
Published: March 16, 2026 at 7:52 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

A Jamhuriyar Congo an kada kuri’a a zaben shugaban kasa ranar Lahadi, wanda ake sa ran zai tsawaita wa’adin mulkin shugaba Denis Sassou Nguesso, daya daga cikin shugabannin Afirka da suka fi dadewa akan karagar mulki, duk kuwa da cewar mutane basu fito da yawaba don kada kuri’unsu.

Sassou na fuskantar wani kalubale daga abokan hamayya, tare da saka wasu fitattun jagororin adawa na kasar a gidan yari, wasu kuma suna gudun hijira. Jam’iyyun adawa da dama sun kauracewa zaben, suna masu cewa tsarin ba shi da inganci.

Fiye da ‘yan Kwango miliyan 3.2 ne aka yi wa rajista don kada kuri’a, ko da yake masu sharhi da kungiyoyin fararen hula sun yi hasashen cewa za a kada kuri’u kusan kashi 68 cikin dari da aka samu a shekarar 2021, lokacin da Sassou ya lashe wa’adinsa na shekaru biyar da suka gabata da kashi 88.4% na kuri’un.

Wani ya shaidawa Reuters cewa, an samu gajerun layuyuka na masu kada kuri’u a mafi akasarin rumfunan zabe a Brazzaville babban birnin kasar.

Bayan da ya kada kuri’arsa a Brazzaville, Sassou ya shaidawa manema labarai cewa yana fatan kwarin gwiwar da ya ce ya gani a fagen yakin neman zabe za ta fito fili a sakamakon karshe.

“Muna fatan abin da na ji a duk lokacin yakin neman zabe zai tabbata a yau,” in ji shi.

Afrika, Labarai, Sauran Duniya, Siyasa

Post navigation

Previous Post: Za’a Jima Ana Fama Da Tsadar Farashin Mai
Next Post: Jagoran Adawar Uganda Bobi Wine Ya Fice Daga Kasar

Karin Labarai Masu Alaka

Zamu Tarwatsa Cibiyoyin Makamashi Da Cibiyoyin Mai Din Iran Amurka
Jirgi Marar Matuki Yayi Ajalin A Kallah Mambobin M23 9 Tare Da Kashe Kakakin Rundunar Afrika
Trump: Isra’ila Ta Daina Kai Hari Ga Duk Cibiyar Iskar Gas Afrika
Turkiyya Ta Zargi Alakar Isra’ila Da Somaliya Afrika
Kurdawa Sun Gargadi ‘Yan Uwansu Game Da Alaka Da Amurka Wajen Yakar Iran Afrika
Kamfanin NNPC Yana Tattaunawa Da Wani Kamfanin Kasar China Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Mutane 13 Sun Mutu Inda Wasu 57 Suka Jikkata A Barundi Afrika
  • APC Ta Sauya Jerin ‘Yan Takararta Bayan Nazarin Ƙorafe-ƙorafen Zaɓen Fidda Gwani Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Ta Samar Da Wuta Mai Aiki Da Hasken Rana A Jami’ar ADUSTECH Afrika
  • Kungiyoyin Mata A Jihar Filato Sunyi Gangamin Samun Jagorancin Siyasa Afrika
  • Indiya Da Brazil Sun Kulla Yarjejeniyar Cinikayya Afrika
  • Kotu Ta Bada Belin Abubakar Malami Bisa Wasu Sharruda Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Shugaba Tinubu Ya Umarci Janye ‘Yan Sanda Masu Gadin Ministoci Tsaro
  • Iran Ta Tsagaita Kai Hare Hare Makwabta Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.