Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Peter Obi Ya Gayyaci Gwamnan Bauchi Bala Abdulkadir Kan Yazo Su Hada Kai Su Gyara Nijeriya. Labarai
  • Tawagar Masu Yi Wa Maniyyata Hidima Za Ta Tashi Zuwa Saudiyya Afrika
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro Labarai
  • Za A Cigaba Da Tattaunawa Domin Kawo Karshen Yakin Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Gwamnatin Najeriya Ta Samar Da Wuta Mai Aiki Da Hasken Rana A Jami’ar ADUSTECH
Published: April 25, 2026 at 4:00 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Gwamnatin Tarayyar Najeriya, ta hannun Hukumar Makamashi ta Kasa (ECN), ta kaddamar da aikin samar da wutar lantarki mai amfani da hasken rana (Solar) mai karfin megawatt biyu (2MW) a Jami’ar Kimiyya da Fasaha ta Aliko Dangote (ADUSTECH) da ke Wudil a Jihar Kano.

Wannan aiki, wanda kudinsa ya kai naira biliyan 3.8, yana karkashin shirin nan na ‘Renewed Hope Solarization’ na gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu. Baya ga aikin samar da wutar, an kuma kaddamar da fitilun kan hanya guda 200 masu amfani da hasken rana a cikin harabar jami’ar.

Darakta Janar na hukumar, Dr. Mustapha Abdullahi, tare da Ministan Kirkira, Kimiyya da Fasaha, Kingsley Tochukwu-Udeh, ne suka kaddamar da fara aikin a ranar Juma’a.

Dr. Abdullahi ya bayyana cewa an ba kamfanin da zai gudanar da aikin wa’adin watanni uku kacal domin kammalawa. Ya ce an tsara wannan aiki ne domin kawo karshen matsalar tsadar wutar lantarki da jami’ar ke fuskanta, inda take biyan naira miliyan 22.4 a kowane wata.

“Wannan aiki na Wudil yana bin sahu ne bayan makamancinsa da muka kaddamar a Asibitin Koyarwa na Aminu Kano a watan Satumban 2025, inda ake sanya tsarin megawatt hudu (4MW), da kuma aikin da muka kaddamar a Jami’ar Bayero ta Kano (BUK) a makon jiya,” in ji Dr. Abdullahi.

Ya kara da cewa an ba kamfanin Safiatu Global Resources Limited kwangilar a kan kudi naira biliyan 3.8, kuma ba za a kara ko sisi a kan kudin ba, sannan dole ne su kammala a cikin lokaci.

Binciken da hukumar ta gudanar ya nuna cewa jami’ar tana da dalibai da ma’aikata sama da 24,000, kuma bukatar wutar da take da ita ta kai tsakanin megawatt 12.3 zuwa 16.4. Sai dai, wutar da take samu daga kamfanonin rarraba wuta ba ta taka kara ta karya ba, yayin da janaretocin da take amfani da su ba sa iya daukar nauyin bukatar jami’ar.

A nasa jawabin, Ministan Kirkira, Kimiyya da Fasaha, Kingsley Tochukwu-Udeh, ya ce wannan aiki mataki ne na raya kasa a karkashin manufofin gwamnatin Tinubu na bunkasa ilimi da kirkire-kirkire ta hanyar samar da ingantaccen makamashi.

Shi ma a nasa bangaren, Shugaban Jami’ar, Farfesa Musa Tukur-Yakasai, ya nuna jin dadinsa da wannan gagarumin tallafi, inda ya ce wannan mataki zai kara bunkasa harkar bincike da koyarwa a jami’ar.

Afrika, Kimiya, Najeriya

Post navigation

Previous Post: Hukumar EFCC Ta Kama Dan Kasuwa A Kamaru

Karin Labarai Masu Alaka

Shugaba Tinubu Ya Gana Da Wasu Gwamnoni Shida Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Kamfanin Bitcoin A Korea Ta Kudu Yayi Kuskuren Turawa Masu Mu’amala Da Kamfanin Kudade Afrika
An Saka Dokar Hana Fita A Jos Ta Arewa Afrika
‘Yan Bindiga Sun Karya Alkawarin Dakatar Da Kai Hare Hare A Najeriya Labarai
Yohanna YD Buru: Makon Haɗin Kan Addinai Ya Ƙarfafa Ilimin Zaman Lafiya A Najeriya Labarai
Shugaba Bola Tinubu Ya Amince Da Inganta Wutan Lantarki A Kasar Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Gwamnatin Najeriya Ta Samar Da Wuta Mai Aiki Da Hasken Rana A Jami’ar ADUSTECH
  • Hukumar EFCC Ta Kama Dan Kasuwa A Kamaru
  • Al’ummar Jihar Nasarawa Suna Cecekuce Bisa Tsaida Aliyu Wadada Takarar Gwamna
  • Gwamnatin Tarayya Tayi Baje Kolin Nasarorin Tinubu
  • Peter Obi Ya Gayyaci Gwamnan Bauchi Bala Abdulkadir Kan Yazo Su Hada Kai Su Gyara Nijeriya.

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Dakarun Sakai A Kasar Sudan Sun Kashe Mutane 28 A Wani Farmaki Afrika
  • Boko Haram Sun Dauke Kansiloli A Borno Tsaro
  • Gwamnatin Najeriya Ta Taya Super Eagles Murnar Lashe Tagulla A Gasar AFCON Wasanni
  • Usman Maiyama Ne Gwarzon Kamun Kifin Argungu Bana Labarai
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Samar Da Tsaro A Jihar Kano Ba Sai An Sa Siyasa Ba! Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Kasashen Thailand Da Cambodia Sun Amince Da Tsagaita Wuta Labarai
  • Kamfanin Dangote Zai Sayo Na’urori Daga Kasar China Kimiya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.