Gwamnatin jihar Katsina ta tabbatar da rasuwar Manjo Janar Rabe Abubakar mai ritaya, wanda ya rasu yayin da yake tsare a hannun ‘yan bindiga bayan sace shi.
A cikin wata sanarwa da Kwamishinan Tsaron Cikin Gida da Harkokin Gida na jihar, Dakta Nasiru Mu’azu, ya fitar, gwamnatin ta bayyana alhininta kan wannan lamari, tana mai cewa rasuwar marigayin babban rashi ne ga iyalansa, Jihar Katsina da kuma Najeriya baki ɗaya.
Sanarwar ta ce marigayin ya rasu ne sakamakon matsalolin rashin lafiya da suka haɗa da ciwon sukari da hawan jini yayin da yake tsare. Ta kuma bayyana cewa gwamnatin jihar tare da hukumomin tsaro sun yi ƙoƙari matuƙa domin ganin an kuɓutar da shi cikin koshin lafiya kafin rasuwarsa.
Gwamnan jihar Katsina, Dikko Umaru Radda, ya miƙa saƙon ta’aziyyarsa ga iyalan marigayin da daukacin al’ummar ƙasar nan, inda ya bayyana lamarin a matsayin wani lokaci na baƙin ciki da ke nuna muhimmancin ƙara haɗa kai wajen yaƙi da matsalar rashin tsaro da ayyukan ‘yan bindiga.
Gwamnan ya kuma jaddada kudirin gwamnatin jihar na ci gaba da aiki tare da Gwamnatin Tarayya da jami’an tsaro domin tabbatar da an hukunta masu hannu a wannan aika-aika tare da ƙarfafa matakan samar da zaman lafiya da tsaro a faɗin jihar.
Gwamnatin Katsina ta kuma tabbatar wa al’umma cewa ba za ta yi ƙasa a gwiwa ba wajen yaƙi da ‘yan bindiga da kuma kare rayuka da dukiyoyin jama’a.
Marigayi Manjo Janar Rabe Abubakar ya kasance ɗaya daga cikin manyan hafsoshin sojin Najeriya da suka yi wa ƙasa hidima tsawon shekaru, kuma za a ci gaba da tunawa da gudunmawar da ya bayar wajen kare martabar ƙasar.


