Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

Janar Rabe Abubakar Ya Mutu A Tsare A Hannun Masu Garkuwa Da Mutane
Published: June 13, 2026 at 7:57 PM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: June 13, 2026

Gwamnatin jihar Katsina ta tabbatar da rasuwar Manjo Janar Rabe Abubakar mai ritaya, wanda ya rasu yayin da yake tsare a hannun ‘yan bindiga bayan sace shi.

A cikin wata sanarwa da Kwamishinan Tsaron Cikin Gida da Harkokin Gida na jihar, Dakta Nasiru Mu’azu, ya fitar, gwamnatin ta bayyana alhininta kan wannan lamari, tana mai cewa rasuwar marigayin babban rashi ne ga iyalansa, Jihar Katsina da kuma Najeriya baki ɗaya.

Sanarwar ta ce marigayin ya rasu ne sakamakon matsalolin rashin lafiya da suka haɗa da ciwon sukari da hawan jini yayin da yake tsare. Ta kuma bayyana cewa gwamnatin jihar tare da hukumomin tsaro sun yi ƙoƙari matuƙa domin ganin an kuɓutar da shi cikin koshin lafiya kafin rasuwarsa.

Gwamnan jihar Katsina, Dikko Umaru Radda, ya miƙa saƙon ta’aziyyarsa ga iyalan marigayin da daukacin al’ummar ƙasar nan, inda ya bayyana lamarin a matsayin wani lokaci na baƙin ciki da ke nuna muhimmancin ƙara haɗa kai wajen yaƙi da matsalar rashin tsaro da ayyukan ‘yan bindiga.

Gwamnan ya kuma jaddada kudirin gwamnatin jihar na ci gaba da aiki tare da Gwamnatin Tarayya da jami’an tsaro domin tabbatar da an hukunta masu hannu a wannan aika-aika tare da ƙarfafa matakan samar da zaman lafiya da tsaro a faɗin jihar.

Gwamnatin Katsina ta kuma tabbatar wa al’umma cewa ba za ta yi ƙasa a gwiwa ba wajen yaƙi da ‘yan bindiga da kuma kare rayuka da dukiyoyin jama’a.

Marigayi Manjo Janar Rabe Abubakar ya kasance ɗaya daga cikin manyan hafsoshin sojin Najeriya da suka yi wa ƙasa hidima tsawon shekaru, kuma za a ci gaba da tunawa da gudunmawar da ya bayar wajen kare martabar ƙasar.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Sauran Duniya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Anyi Jana’izar Dan Majalisar Wakilai Yaya Bauchi Tongo
Next Post: Ahmed Gara Ya Kaddamar da Kofin Sarkin Gombe, Ya Jaddada Bunƙasa Matasa

Karin Labarai Masu Alaka

Kasar Habasha Da Turkiyya Sun Kulla Yarjejeniyar Makamashi Afrika
Rundunar ‘Yan Sandan Kebbi Ta Dakile Yunkurin Garkuwa Da Mutune, Ta Kama Masu Laifi Afrika
Najeriya Da Amurka Sun Amince Su Haɗa Kai Don Inganta ’Yancin Addini Da ƙarfafa Tsaro A Nijeriya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Kamfanin Dangote Zai Sayo Na’urori Daga Kasar China Kimiya
Kamfanin Magani Na Aspen Yayi Gagarumar Asara A Cinikayya Afrika
Hukumar NDLEA Ta Kama Miyagun Kwayoyi A Edo Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Hukumar ICPC Ta Kwato Makudan Kudade Rediyo
  • Nasarawa United Ta Kai Wasan Kusa da Ƙarshe Na Gasar Gusau/Ahlan 2026 Wasanni
  • Shirin Safe 0500 UTC Yau Asabar 11.22.2025 Rediyo
  • Jirgin Hakar Mai Daga Turkiyya Ya Isa Mugadishu Afrika
  • Wani Ya Yiwa ‘Yar Sa Mai Shekaru 8 Fyade A Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Tattaunawar Nukiliya Tsakanin Iran Da Amurka Yana Tasirin Akan Farashin Albarkatun Mai Amurka
  • Harkar Zirga Zirgar Jiragen Sama Ya Bunkasa A Kenya Afrika
  • Zamu Hada Kai Mu Yaki Cutar Shan’inna (Polio) Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.