Gwamnatin Jamhuriyar Nijar ta kafa sabuwar doka da ta haramta luwadi, madigo da kuma duk wata alaƙa ta aure tsakanin masu jinsi guda, tare da tanadar hukunci mai tsauri ga duk wanda aka samu da laifin karya dokar.
Dokar, wadda shugaban ƙasar, Janar Abdourahamane Tiani, ya sanya wa hannu, ta tanadi tarar kuɗi har zuwa CFA miliyan 100 da kuma ɗaurin shekaru aƙalla 20 a gidan yari ga duk wanda aka samu da aikata irin waɗannan laifuka.
Matakin ya zo ne a yayin da ake samun rahotannin cewa hukumomin ƙasar na gudanar da bincike kan wasu mutane da dama da ake zargi da hannu a ayyukan da dokar ta haramta. Rahotannin sun kuma nuna cewa wasu daga cikin waɗanda ake binciken manyan ma’aikatan gwamnati ne.
Sai dai har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto, hukumomin Nijar ba su fitar da wata sanarwa a hukumance da ke bayyana cikakken bayani kan binciken da ake yi ko kuma adadin mutanen da abin ya shafa ba.
Masu lura da al’amuran siyasa da zamantakewa na ganin wannan mataki wani muhimmin sauyi ne a tsarin dokokin ƙasar, wanda ka iya jawo martani daga ƙungiyoyin kare haƙƙin ɗan Adam da sauran masu ruwa da tsaki a cikin gida da wajen Nijar.
A halin yanzu, gwamnati ba ta bayyana cikakkun matakan aiwatar da sabuwar dokar ba, yayin da ake ci gaba da sa ido kan yadda lamarin zai kasance a nan gaba.


