Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19 Afrika
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027 Afrika
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki Afrika
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko Afrika

Fubara Yana Yiwa Dimokraɗiyya Zagon Kasa
Published: January 9, 2026 at 7:30 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Kakakin majalisar dokokin jihar Rivers a Najeriya, Martins Amaewhule, ya zargi gwamna Siminalayi Fubara da tauye tafiyar dimokuraɗiyya a jihar.

Amaewhule ya yi wannan zargi ne a ranar Alhamis, jim kaɗan bayan majalisar ta fara shirin tsige gwamnan da mataimakiyarsa, Ngozi Odu, bisa zargin aikata manyan laifuka.

A cewar kakakin, ɓangaren zartarwa na gwamnati ya kasa bin tanade-tanaden kundin tsarin mulki sau da dama, musamman dangane da gabatar da kasafin kuɗi da amincewa da kashe kuɗaɗe.

“Babu wani abu da ke hana gwamnati gabatar da kasafin kuɗi da gangan ya zaɓi ƙin yin hakan,” in ji Amaewhule.

Ya ce gwamnan na faɗa wa magoya bayansa cewa wannan majalisa ba ta da wani ƙarfi, yana kiranta da “kare mara haƙora”, yana kuma cewa Majalisar Dokoki ta 10 ba za ta iya yin komai ko tilasta bin kundin tsarin mulki ba.

Amaewhule ya bayyana lamarin a matsayin mai haɗari ga dimokuraɗiyya a jihar Rivers.

“Wannan abin takaici ne ga dimokuraɗiyyarmu, Sir Siminalayi Fubara da Farfesa Ngozi Odu barazana ne ga dimokuraɗiyyarmu kuma idan aka bar su suka ci gaba da wannan hali, ina fargabar abin da zai faru da tafiyar dimokuraɗiyya a jihar Rivers,” in ji shi.

Ya kuma zargi gwamnan da mataimakiyarsa da kashe kuɗaɗen jama’a ba tare da amincewar Majalisa ba.

“Suna yawo daga wuri zuwa wuri suna kashe kuɗaɗen masu biyan haraji ba tare da amincewar majalisa ba,” in ji Amaewhule.

Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya

Post navigation

Previous Post: Barau Jibril: Mu Ba ‘Yan Amshin Shata Bane A Majalisa
Next Post: Gwamnatin Jihar Gombe Ta Haramta Sana’ar Bola Jari

Karin Labarai Masu Alaka

Rundunar ‘Yan Sandan Gombe Ta Kuɓutar da Yaro Daga Hannun Masu Garkuwa Afrika
CAN: Da Alamu Daliban St. Mery Na Cikin Koshin Lafiya Najeriya
Jami’an Tsaro: Babu Abun Tashin Hankali Kan Shawagin Jiragen Amurka Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Shugaba Tinubu Ya Isa Legas Domin Hutun Karshen Shekara Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Jagoran Kasar Iran Yace Basa Bukatar Tallafin Kasar Amurka Afrika
Gwamnan Gombe Ya Yaba Da Hikima Da Jagorancin Sarkin Gombe A Shekaru 12 Na Jagoranci Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Ma’aikatan Tattara Kudin Haraji Sunyi Rikici Da Masu Babura A Bauchi Najeriya
  • Rundunar ‘Yan Sandan Gombe Ta Kuɓutar da Yaro Daga Hannun Masu Garkuwa Afrika
  • Aikin Layin Dogon Kasar Uganda Zai Hade Kasar Da Tanzania Da Kwango Kimiya
  • Eberechi Eze Ba Zai Buga Wasannin Da Ingila Za Tayiba Arteta Wasanni
  • Kamfanin Dangote Zai Sayo Na’urori Daga Kasar China Kimiya
  • Gwamnatin Jihar Kano Zata Kashe Makudan Kudade Ga Jama’ar Kano! Najeriya
  • AFCON 2025, Jerin Abubuwan Da Aka Haramta Wa Magoya Baya Wasanni
  • Rundunar Operation Endurance Peace Ta Gano Wajen Kera Makamai A Jihar Filato Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.