Tinubu ya isa Lagos domin hutun Kirsimeti da Sabuwar Shekara.
Shugaban ƙasar Najeriya Bola Tinubu ya isa jihar Lagos domin yin hutun Kirsimeti da Sabuwar Shekara, bayan kammala ziyarar aiki da ya kai jihohin Borno da Bauchi.
A lokacin ziyarar sa, Tinubu ya ƙaddamar da ayyuka a Borno, ya halarci bikin aure a Maiduguri, sannan ya kai ziyarar ta’aziyya a Bauchi ga iyalan marigayi Sheikh Dahiru Bauchi.
A Lagos, ana sa ran Shugaban ƙasar zai halarci bikin Eyo Festival a ranar 27 ga Disamba a matsayin Babban Baƙo na musamman.


