Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Jami’an ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayi Afrika
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai Afrika
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari Afrika
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe Afrika
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS Afrika

Masu Kare Hakkin ‘Yan Gudun Hijira A Amurka Sun Mika Koke
Published: January 23, 2026 at 8:32 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Masu rajin kare hakkin ‘yan gudun hijira sun mika takaddar koke zuwa kotu don dakatar da kudurin gwamnatin shugaba Donald Trump na soke damar samun mafaka, da bada izinin zama da aka bawa dubbannan ‘yan kasar Ethiopia da ke zaune Amurka.

Wasu ‘yan kasar Ethiopia 3, tare da kungiyar masu rajin kare hakki ta mazauna ‘yan Afirka sun gabatar da kara a wata babbar Kotun kasa da ke birnin Boston na jihar Massachusettes, ranar Alhamis cewa Ma’aikatar Tsaron Cikin gida ta Amurka tana neman salwantarwa da mutane fiye da dubu biyar damar da suke da shi na samun mafaka ta wucin gadi ba bisa ka’ida ba. Sun ce ma’aikatar na nema ta sa mutanen su rasa mafakar su bayan 13 ga watan Fabrairu.

Sun ce duk da kasar ta Ethiopia har yanzu tana cikin halin dake barazana ga rayukan mutane, sakatariyar tsaron cikin gida Kristi Noem ta soke mafakar da Amurka ta bawa ‘yan Ethiopian ba bisa ka’ida ba, kuma ta basu wa’adin kwana 60 kacal.

Wannan na daga cikin korafe korafe na kwanan nan da ake kaiwa gaban kotu don kalubalantar yunkurin gwamnatin Trump, na dakile mafaka da mutane ke da shi, da ake yiwa ‘yan asalin wasu kasashe da dama.

A tsarin dokar kasa, ana bawa mutanen da kasashen su ke fama da gurbacewar yanayi, yaki, ko wasu abubuwan da ka iya kawo barazana ga rayuwar al’umma. Ana bawa ‘yan gudun hijira da suka cancanta takardun damar samun aiki, kuma a basu mafaka ta wucin gadi, da zata tsare su daga fuskantar kora daga kasa.

An sha kawowa kotu korafi don kalubalantar neman korar mutane da suka fito daga wasu kasashe da suka hada da Sham, Venezuela, Haiti, Nicaragua, da kuma Sudan ta Kudu, inda ake samu kotu ta dakatar ko ta hana gwamnatin ta Trump soke takardun zama na mutanen.

Amurka

Post navigation

Previous Post: Amurka Tafara Yiwa Kasar Iraq Barazana
Next Post: An Yiwa Dokokin Kare Hakkin Yara Rikon Sakainar Kashi

Karin Labarai Masu Alaka

Shugaban Kasar Ghana Ya Soki Manufofin Gwamnatin Amurka Afrika
Farashin Mai Ya Doshi Dala 100 Kowacce Ganga Afrika
Farashin Dalar Amurka Ya Tashi Ranan Juma’a Amurka
Babban Sakataren MDD Yayi Allah Wadai Da Matakin Soja A Gabas Ta Tsakiya Afrika
Rasha Ta Gargadi Amurka Da Isra’ila Kan Harin Iran Afrika
Wani Bincike Ya Nuna Cewar Da Wuya Iran Ta Bude Mashigin Hormuz Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jami’an ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayi
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • ‘Yan Ta’adda Sun Hallaka Malaman Makaranta A Tilabery Afrika
  • Jihar Gombe Ta Saka Hannu Kan Yarjejeniya Da Kamfanonin Tunisiya Kimiya
  • Farashin Danyen Mai A Amurka Ya Tashi Afrika
  • Iran Zata Mayarwa Amurka Martani Amurka
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Matasa Sun Sayawa Ferfesa Pantami Fom Din Takarar Gwamnan Gombe Afrika
  • Gwamnatin Amurka Da Najeriya Sunyi Hadakar Inganta Asibiticin Kiristoci Amurka
  • An Canza Shugabannin Hukumar Hakar Ma’adanai A Congo Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.