Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

Masu Kare Hakkin ‘Yan Gudun Hijira A Amurka Sun Mika Koke
Published: January 23, 2026 at 8:32 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Masu rajin kare hakkin ‘yan gudun hijira sun mika takaddar koke zuwa kotu don dakatar da kudurin gwamnatin shugaba Donald Trump na soke damar samun mafaka, da bada izinin zama da aka bawa dubbannan ‘yan kasar Ethiopia da ke zaune Amurka.

Wasu ‘yan kasar Ethiopia 3, tare da kungiyar masu rajin kare hakki ta mazauna ‘yan Afirka sun gabatar da kara a wata babbar Kotun kasa da ke birnin Boston na jihar Massachusettes, ranar Alhamis cewa Ma’aikatar Tsaron Cikin gida ta Amurka tana neman salwantarwa da mutane fiye da dubu biyar damar da suke da shi na samun mafaka ta wucin gadi ba bisa ka’ida ba. Sun ce ma’aikatar na nema ta sa mutanen su rasa mafakar su bayan 13 ga watan Fabrairu.

Sun ce duk da kasar ta Ethiopia har yanzu tana cikin halin dake barazana ga rayukan mutane, sakatariyar tsaron cikin gida Kristi Noem ta soke mafakar da Amurka ta bawa ‘yan Ethiopian ba bisa ka’ida ba, kuma ta basu wa’adin kwana 60 kacal.

Wannan na daga cikin korafe korafe na kwanan nan da ake kaiwa gaban kotu don kalubalantar yunkurin gwamnatin Trump, na dakile mafaka da mutane ke da shi, da ake yiwa ‘yan asalin wasu kasashe da dama.

A tsarin dokar kasa, ana bawa mutanen da kasashen su ke fama da gurbacewar yanayi, yaki, ko wasu abubuwan da ka iya kawo barazana ga rayuwar al’umma. Ana bawa ‘yan gudun hijira da suka cancanta takardun damar samun aiki, kuma a basu mafaka ta wucin gadi, da zata tsare su daga fuskantar kora daga kasa.

An sha kawowa kotu korafi don kalubalantar neman korar mutane da suka fito daga wasu kasashe da suka hada da Sham, Venezuela, Haiti, Nicaragua, da kuma Sudan ta Kudu, inda ake samu kotu ta dakatar ko ta hana gwamnatin ta Trump soke takardun zama na mutanen.

Amurka

Post navigation

Previous Post: Amurka Tafara Yiwa Kasar Iraq Barazana
Next Post: An Yiwa Dokokin Kare Hakkin Yara Rikon Sakainar Kashi

Karin Labarai Masu Alaka

Shugaba Putin Ya Bukaci Kawo Karshen Yaki Da Iran Afrika
Kotun Amurka Tana Tuhumar Wani Dan Jarida Amurka
Kwararru Sun Nuna Damuwa Game Da Yakin Iran Amurka
Sabon Ma’aikacin Tsaro Ne Ya Kashe Amurkawa Amurka
Farmakin Da Aka Kai Makarantar Mata A Iran Yayi Ajalin Yara Da Dama Afrika
Isra’ila Ta Kai Hari Cibiyar Makamashin Nukiliyar Iran Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Shugaba Tinubu Ya Umarci Janye ‘Yan Sanda Masu Gadin Ministoci Tsaro
  • Kasar Saudiya Zata Cika Azumi Talatin Kimiya
  • Dangote Ya Rage Farashin Mai A Najeriya Labarai
  • Farashin Kasuwar Yawon Bude Ido A Kasuwar Hannayen Jari Ya Fadi Afrika
  • Karamar Sallah: Hukumar Kashe Gobara A Gombe Ta Kuduri Aniyar Kare Al’umma Afrika
  • Hafsan Sojin Najeriya: Samar Da Sabbin Wajen Horas Da Sojoji Zai Inganta Tsaro Tsaro
  • Mizanin Tattalin Arzikin Najeriya Na 2024 Ya Karu Da Kashi 3.84% Labarai
  • Harin ‘Yan Daba Ya Hallaka Mutane 70 A Kasar Haiti Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.