Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojoji Sun Ceto Mutane 23, Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 19 A Cikin Sa’o’i 24 Afrika
  • 3G Taskforce Ya Dasa Bishiyoyi Don Kare Muhalli A Gombe Afrika
  • Builder Mahmood Yusuf Ya Tallafa Wa Mata Da Matasa Afrika
  • Gwamnan Jihar Bauchi Ya Jagoranci Tsohon Shugaban Kasar Najeriya Rangadi A Bauchi Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Amince Da Naɗin Manyan Sakatarori 19 Afrika

Masu Kare Hakkin ‘Yan Gudun Hijira A Amurka Sun Mika Koke
Published: January 23, 2026 at 8:32 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Masu rajin kare hakkin ‘yan gudun hijira sun mika takaddar koke zuwa kotu don dakatar da kudurin gwamnatin shugaba Donald Trump na soke damar samun mafaka, da bada izinin zama da aka bawa dubbannan ‘yan kasar Ethiopia da ke zaune Amurka.

Wasu ‘yan kasar Ethiopia 3, tare da kungiyar masu rajin kare hakki ta mazauna ‘yan Afirka sun gabatar da kara a wata babbar Kotun kasa da ke birnin Boston na jihar Massachusettes, ranar Alhamis cewa Ma’aikatar Tsaron Cikin gida ta Amurka tana neman salwantarwa da mutane fiye da dubu biyar damar da suke da shi na samun mafaka ta wucin gadi ba bisa ka’ida ba. Sun ce ma’aikatar na nema ta sa mutanen su rasa mafakar su bayan 13 ga watan Fabrairu.

Sun ce duk da kasar ta Ethiopia har yanzu tana cikin halin dake barazana ga rayukan mutane, sakatariyar tsaron cikin gida Kristi Noem ta soke mafakar da Amurka ta bawa ‘yan Ethiopian ba bisa ka’ida ba, kuma ta basu wa’adin kwana 60 kacal.

Wannan na daga cikin korafe korafe na kwanan nan da ake kaiwa gaban kotu don kalubalantar yunkurin gwamnatin Trump, na dakile mafaka da mutane ke da shi, da ake yiwa ‘yan asalin wasu kasashe da dama.

A tsarin dokar kasa, ana bawa mutanen da kasashen su ke fama da gurbacewar yanayi, yaki, ko wasu abubuwan da ka iya kawo barazana ga rayuwar al’umma. Ana bawa ‘yan gudun hijira da suka cancanta takardun damar samun aiki, kuma a basu mafaka ta wucin gadi, da zata tsare su daga fuskantar kora daga kasa.

An sha kawowa kotu korafi don kalubalantar neman korar mutane da suka fito daga wasu kasashe da suka hada da Sham, Venezuela, Haiti, Nicaragua, da kuma Sudan ta Kudu, inda ake samu kotu ta dakatar ko ta hana gwamnatin ta Trump soke takardun zama na mutanen.

Amurka

Post navigation

Previous Post: Amurka Tafara Yiwa Kasar Iraq Barazana
Next Post: An Yiwa Dokokin Kare Hakkin Yara Rikon Sakainar Kashi

Karin Labarai Masu Alaka

Sakataren Kungiyar NATO Yayi Magana Da Hukumomin Kasashe Afrika
Kasashen Amurka,Israela Da Iran Sun Amince Da Dakatar Da Yaki Afrika
Dakarun Sojin Amurka Sunfara Sauka A Najeriya Amurka
‘Yan Sanda A Tsibirin Bahamas Sun kama Mijin Wata Ba Amurkiya Amurka
Gwamnatin Trump Ta Karawa Iran Wasu Takunkumai Amurka
Shugaba Donald Trump Yabada Umarnin Hana Jiragen Dakon Mai Shiga Venezuela Amurka

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojoji Sun Ceto Mutane 23, Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 19 A Cikin Sa’o’i 24
  • 3G Taskforce Ya Dasa Bishiyoyi Don Kare Muhalli A Gombe
  • Builder Mahmood Yusuf Ya Tallafa Wa Mata Da Matasa
  • Trump Ya Yi Gargadi Kan Shirin Cire Shugaban FIFA Infantino
  • Katsina United Ta Yi Jimamin Mutuwar Ɗan Wasanta Ozoh

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Gobara Ta Tashi A Hukumar FIRS Dake Abuja Najeriya
  • Mayakan RSF Sun Zafafa Kai Hare Hare Da Jirgi Maras Matuki A Sudan Labarai
  • Hawan Babbar Sallah A Masarautar Kaltungo Dake Jihar Gombe Afrika
  • Tsohon Lauyan Amurka Jack Smith Ya Fadi Maganganu Game Da Donald Trump Amurka
  • Kungiyar Kwadago Ta NLC Ta Gudanar Da Zanga-Zanga Bisa Matsalar Tsaro Tsaro
  • Yawan wadanda suka mutu a mummunan harin yanbindiga a Jihar kwaran Najeriya yakai 170 Najeriya
  • Tattalin Arzikin Najeriya Ya Farfardo Bisa Samun Wasu Sauye Sauye Labarai
  • Amurka Na Shirin Kauracewa Taron Kungiyar Kasashen G20 Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.