Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Yau Shekaru 60 Da Kisan Gilla Ga Sir. Ahmadu Bello Sardaunan Sakkwato
Published: January 15, 2026 at 8:48 PM | By: Yusuf Aliyu Harande | Updated: January 15, 2026

Yau a ke cika shekaru 60 da yin kisan gilla ga Firimiyan Arewa Sir Ahmadu Bello Sardaunan Sokoto a juyin mulkin soja na farko a Najeriya.

Wasu hafsoshin soja daga akasari kabilar Igbo ne su ka aiwatar da juyin mulkin ranar 15 ga Janairu 1966.

Shi dai wannan juyin mulkin da ya haddasa zubar da jini ya yi sanadiyyar kisan gilla ga Firimiyan Arewa Sir Ahmadu Bello, Firaministan Najeriya Sir Abubakar Tafawa Balewa da Firimiyan kudu maso yamma Chief Ladoke Akintola a birnin Badun.

Juyin mulkin ya shafi manyan ‘yan siyasar Arewa da kuma Chief Akintola na Yarbawa amma bai taba kabilar Igbo ba.

Chukwuma Nzeogwu wanda hafsan soja ne da ya ci alfarmar Sardauna shi ya shiga gidan Firimiya ya yi ma sa kisan gilla shi da matarsa Hafsa da ta yi kokarin tare albarushi.

Nzeogwu ya nuna farin ciki da kisan da kuma mubaya’arsa ga Janar Johnson Aguiyi Ironsi wanda ya haye madafun iko a wannan yanayi na zubar da jini.

An tabbatar kalaman Sir Ahmadu Bello kan shirin ba wa al’ummar Arewa fifiko su amshi guraben ayyukan lardinsu da kaucewa babakeren Igbo ya zama daga dalilan kisan.

Dattijon NEPU da ta yi adawa da jam’iyyar NPC ta Sardauna Alhaji Hussaini Gariko ya ce adalcin Sardauna da amanarsa ababen koyi ne ga dukkan jagororin al’ummarmu.

Bayan kisan gilla Sardauna da Firaministan Najeriya Sir Abubakar Tafawa Balewa, Janar Johnson Aguiyi Ironsi ya hau karaga amma kimanin wata 6 da kwana 15 a ka kifar de gwamnatinsa kuma har daga bisani ya kai ga yakin basasar Najeriya yayin da gwamnan Soja na jihar kudu maso gabar Odumegwu Ojukwu ya ayyana ballewa daga Najeriya.

Dakarun gwamnatin tarayya sun fafata tun daga 1967-1970 har su ka yi nasarar sake hade kasar.

Har yanzu Najeriya ba ta warware daga fitinar juyin mulkin 1966 ba.

https://gtahausa.com/wp-content/uploads/2026/01/AS-SARDAUNAS-ASSASSAINATION-CLOCKS-60-YEARS.mp3
Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Post navigation

Previous Post: Amurka Ta Janye Sojojinta Daga Gabas Ta Tsakiya
Next Post: Tattalin Arzikin Najeriya Ya Farfardo Bisa Samun Wasu Sauye Sauye

Karin Labarai Masu Alaka

Anyi Girgizar Kasa Mai Karfi A Kasar Mexico Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Kotun Tarayya Ta Yankewa Nnamdi Kanu Daurin Rai-da-Rai Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Gwamnonin Arewa “Mun Amince Da Samar Da ‘Yan Sandan Jihohi” Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Anyi Sallar Rokon Ruwa A Saudiya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
CAF Ta Yanke Hukunci Kan Ƙasashen Senegal Da Moroko AFCON 2025 Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Shugaba Tinubu Ya Isa Legas Domin Hutun Karshen Shekara Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Kungiyar Mata Manoma A Najeriya Ta Raba Kyautar Abinci A Gombe
  • Ambaliyar Ruwa Yayi Ajalin Mutane A Nairobi
  • ‘Yan Sandan Najeriya Sunyi Nasarar Hallaka ‘Yan Ta’adda A Katsina
  • Iran Ta Tsagaita Kai Hare Hare Makwabta
  • Shugaban Amurka Ya Ya Bukaci Iran Ta Mika Wuya

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Pakistan Da Afghanistan Sun Shiga Kwana Na Biyar Suna Fafatawa Afrika
  • Kasar Colombia Tare Da Amurka Zasu Fitar Da Man Venezuela Labarai
  • Muhawara Mai Zafi Tsakanin APC da ADC Shirye-Shirye
  • Sabon Ma’aikacin Tsaro Ne Ya Kashe Amurkawa Amurka
  • Guterres: Babban Kuskure Ne Yadda Isra’ila Ta Kai Farmaki A Gaza Labarai
  • Malaman Addinin Musulunci Da Kirista Sunyi Bikin Cika Shekara 15 Na Iftar A Najeriya Afrika
  • An Tsinci Gawar Yarinya A Gombe Najeriya
  • Rundunar Hadinkan Saudiya Tayi Ikirarin Mayar Da Martani Ga ‘Yan Aware Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.