Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

Yau Shekaru 60 Da Kisan Gilla Ga Sir. Ahmadu Bello Sardaunan Sakkwato
Published: January 15, 2026 at 8:48 PM | By: Yusuf Aliyu Harande | Updated: January 15, 2026

Yau a ke cika shekaru 60 da yin kisan gilla ga Firimiyan Arewa Sir Ahmadu Bello Sardaunan Sokoto a juyin mulkin soja na farko a Najeriya.

Wasu hafsoshin soja daga akasari kabilar Igbo ne su ka aiwatar da juyin mulkin ranar 15 ga Janairu 1966.

Shi dai wannan juyin mulkin da ya haddasa zubar da jini ya yi sanadiyyar kisan gilla ga Firimiyan Arewa Sir Ahmadu Bello, Firaministan Najeriya Sir Abubakar Tafawa Balewa da Firimiyan kudu maso yamma Chief Ladoke Akintola a birnin Badun.

Juyin mulkin ya shafi manyan ‘yan siyasar Arewa da kuma Chief Akintola na Yarbawa amma bai taba kabilar Igbo ba.

Chukwuma Nzeogwu wanda hafsan soja ne da ya ci alfarmar Sardauna shi ya shiga gidan Firimiya ya yi ma sa kisan gilla shi da matarsa Hafsa da ta yi kokarin tare albarushi.

Nzeogwu ya nuna farin ciki da kisan da kuma mubaya’arsa ga Janar Johnson Aguiyi Ironsi wanda ya haye madafun iko a wannan yanayi na zubar da jini.

An tabbatar kalaman Sir Ahmadu Bello kan shirin ba wa al’ummar Arewa fifiko su amshi guraben ayyukan lardinsu da kaucewa babakeren Igbo ya zama daga dalilan kisan.

Dattijon NEPU da ta yi adawa da jam’iyyar NPC ta Sardauna Alhaji Hussaini Gariko ya ce adalcin Sardauna da amanarsa ababen koyi ne ga dukkan jagororin al’ummarmu.

Bayan kisan gilla Sardauna da Firaministan Najeriya Sir Abubakar Tafawa Balewa, Janar Johnson Aguiyi Ironsi ya hau karaga amma kimanin wata 6 da kwana 15 a ka kifar de gwamnatinsa kuma har daga bisani ya kai ga yakin basasar Najeriya yayin da gwamnan Soja na jihar kudu maso gabar Odumegwu Ojukwu ya ayyana ballewa daga Najeriya.

Dakarun gwamnatin tarayya sun fafata tun daga 1967-1970 har su ka yi nasarar sake hade kasar.

Har yanzu Najeriya ba ta warware daga fitinar juyin mulkin 1966 ba.

https://gtahausa.com/wp-content/uploads/2026/01/AS-SARDAUNAS-ASSASSAINATION-CLOCKS-60-YEARS.mp3
Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Post navigation

Previous Post: Amurka Ta Janye Sojojinta Daga Gabas Ta Tsakiya
Next Post: Tattalin Arzikin Najeriya Ya Farfardo Bisa Samun Wasu Sauye Sauye

Karin Labarai Masu Alaka

Gombe Ta Yi Gasar Makarantun Firamare Don Bikin Cika Shekaru 100 Na Hassan Central Afrika
Gangamin Wayar Da Kai Don Kawo Karshen Cin Zarafin Jinsi A Jihar Gombe Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Wani Jirgin Kasa Yayi Hatsari A Kudancin Spain Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Kano: Gwamna Abba Kabir Yusuf Ya Amince da Garo A Matsayin Mataimakinsa Na 2027 Afrika
Ferfesa Pantami Yayi Watsi Da Amincewa Da Jamilu Isiyaku Gwamna Afrika
Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Kasar Botswana Na Samun Kudaden Shiga Da Lu’ulu’u Labarai
  • Sanata Sa’idu Alkali Ya Kaurace Wa Zaben Fidda Gwani Afrika
  • Gwamnan Jihar Kebbi Ya Amince Da Biyan Hakkokin Tsofin Ma’aikata 800 Labarai
  • Boko Haram Sun Farmaki Sansanin Sojoji A Borno Tsaro
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kamallah Jigilar Alhazain Najeriya Domin Hajjin 2026 Afrika
  • Mataimakin Shugaban Amurka Ya Sauka A Islamabad Domin Tattaunawa Afrika
  • Gobara Ta Tashi A Hukumar FIRS Dake Abuja Najeriya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.