Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Rundunar ‘Yan Sandan Gombe Ta Kuɓutar da Yaro Daga Hannun Masu Garkuwa Afrika
  • Tinubu Ya Buɗe Katafaren Kamfanin Sarrafa Lithium Domin Bunƙasa Tattalin Arziki Afrika
  • Sojoji Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 1,597, Sun Ceto Mutane 1,516 – DHQ Afrika
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u Afrika
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa Afrika

Ahmed Musa, Yayi Ritaya A ƙwallon ƙasa Da ƙasa
Published: December 17, 2025 at 3:29 PM | By: Bala Hassan | Updated: December 17, 2025

Tsohon kyaftin ɗin Super Eagles Ahmed Musa ya sanar da yin ritaya daga ƙwallon ƙafa ta ƙasa da ƙasa, wanda hakan ya kawo ƙarshen shekaru 15 da ya shafe yana wasa wa ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Najeriya.

Musa ya sanar da hakan ne a ranar Laraba ta shafin X ɗinsa a hukuma, yana mai bayyana shawarar tasa ta biyo bayan la’akari da ya yi sosai, ya ce sanya rigar kore da fari idan ya tuna abu ne mai ma’ana sosai a gare shi.

Na tuna lokacin da na fara tafiya ta ƙasa da ƙasa a matsayin matashin ɗan wasa, lokacin da aka gayyace ni zuwa ƙungiyoyin ƙasa na ‘yan ƙasa da shekaru 20, da 23 da manyan ƙungiyoyi, ban taba yin jinkirin zuwa Najeriya ba” in ji shi.

Musa ya ya buga wasanni 111 a ƙungiyar Super Eagles, wanda hakan ya sa ya zama ɗan wasa mafi buga wasa a tarihin ƙwallon ƙafa ta ƙasar.

Ya samu nasarar lashe gasar cin kofin ƙasashen Afirka ta 2013 kuma ya ci gaba da zama ɗan wasan da ya fi zura ƙwallo a Najeriya a gasar cin kofin duniya ta FIFA, inda ya zura ƙwallaye masu kyau a kan Argentina a 2014 da Iceland a 2018.

Ya bayyana cimma wasanni 111 a matsayin babban abin farin ciki da girmamawa ne a koyaushe.

Musa ya ƙara da cewa lashe gasar AFCON ta 2013 wani muhimmin abu ne, zaman kyaftin ɗin ƙungiyar ya koya masa darussa masu mahimmanci game da shugabanci, haƙuri da kuma sanya wasu a gaba.

Babban Manaja kuma ɗan wasan ƙungiyar Kano Pillars ya gode wa abokan aikinsa, masu horarwa, da duk ma’aikatan da kuma masu kula da ƙwallon ƙafa saboda goyon bayan da suka ba shi na tsawon shekaru.

Ya kuma nuna matuƙar godiya ga magoya bayan Najeriya na gida da waje saboda alakar da sukayi da shi a tsawon aikinsa.

Ya kammala da cewa ya ba da dukkanin iyawarsa ga Najeriya kuma yana da kwarin gwiwa game da makomar Super Eagles, ya ƙara da cewa dangantakarsa da ƙasar za ta ci gaba.

Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Wasanni

Post navigation

Previous Post: Shugaban Kasar Amurka Yakara Hana Wasu Kasashe Shiga Amurka Ciki Harda Nijar
Next Post: Ana Cigaba Da Kai Kayan Agaji Kasar Morocco Sakamakon Tsananin Hunturu

Karin Labarai Masu Alaka

Matatar Man Dangote Zata Wadatar Da Najeriya Da Makota Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Farashin Mai Ya Fadi Fiye Da Dala Daya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Gwamna Inuwa Yahaya Ya Bukaci Al’ummar Gombe Su Haɗa Kai Wajen Yaƙi Da Ta’addanci Afrika
Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Magoya Bayan Nice Sun Kai Hari Wa ‘Yan Wasansu Wasanni
An Gudanar Da Taron Matasan Kasashe 6, Don Kawo Karshen Ta’addanci Wasanni

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Rundunar ‘Yan Sandan Gombe Ta Kuɓutar da Yaro Daga Hannun Masu Garkuwa
  • Tinubu Ya Buɗe Katafaren Kamfanin Sarrafa Lithium Domin Bunƙasa Tattalin Arziki
  • Sojoji Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 1,597, Sun Ceto Mutane 1,516 – DHQ
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Sojin Najeriya Da ‘Yan Ta’adda Sunyi Taho Mugama Najeriya
  • Gwamnan Jihar Gombe Ya Umurci A Rufe Makarantu Labarai
  • Kamfanin NNPC Yana Tattaunawa Da Wani Kamfanin Kasar China Labarai
  • An Bukaci Sabbin Shugabanni Su Yi Jagoranci Nagari da Inganta Ayyukan Jama’a Labarai
  • Masu Luwadi Na Fuskantar Tara Da Daurin Shekaru 20 A Nijar Afrika
  • Wani Bincike Ya Nuna Cewar Da Wuya Iran Ta Bude Mashigin Hormuz Afrika
  • Za’a Saka Tarihin Trump A Manhajar Makarantu Don Jajircewasa Da Kwazo Amurka
  • Shugaba Tinubu Yace Bazai Bawa ‘Yan Najeriya Kunya Ba Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.