Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

Matatar Man Dangote Zata Wadatar Da Najeriya Da Makota
Published: December 1, 2025 at 9:45 PM | By: Yusuf Aliyu Harande

A Najeriya kamfanin tace man fetur na Dangote, ya fada yau Litinin yana iya samarda man fetur lita bilyan daya da rabi ako wani wata. Daga nan ya gayyaci hukumomin kula da samar  da man fetur a kasar su ziyarci kamfanin don su gasgata, bayanda sashen ya wallafa alkaluma da suke nuna cewa, matatar man fetur yana samar da kashi daya cikin uku na wannan adadi.

Maganganu da ake yi cewa matatun mai da suke kasar basa iya samar da wadataccen mai da Najeriya take bukata, yana daga cikin dalilan da suka sa gwamnati ta dakatar da hana shigo da tataccen mai daga ketare.

Hukumomin kasar dake sa ido sun ce Najeriya tana bukatar litan mai milyann 55 a kowace rana, ko litan mai bilyan daya da digo 67 ako wani wata.

Kamfanin yace Mai da suke samarwa a Dangote “a shirye su ke kuma suna da karfin” samarda tataccen mai lita bilyan daya da rabi a cikin watan nan na Disamba, da kuma watan Janairu, daga bisani kuma zai iya samarda litan mai bilyan daya da digo bakwai a watan Febwairu har sai yadda hali yayi.

Kamfanin matatar mai na Dangoten yace domin kaucewa duk wata kumbiya kumbiya ya gayyaci hukumomin kasar dake sa ido kan samar da man fetur su taho matatar Man daga yau daya ga watan Disamba, su wallafa alkaluman abunda matattar Man take sarrafawa ako wace rana kuma ta fadawa duniya.

Ahalinda ake ciki kuma, tattalin arzikin Najeriya ya habaka da kusan kashi hudu a cikin wata uku daga Yuli zuwa Satumba, a bangarorin da basu shafi Mai ba.

Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Post navigation

Previous Post: Jihohin Arewaci Sun Kafa Asusun Yaki Da Ta’addanci
Next Post: Ministan Tsaron Najeriya Badaru Yayi Murabus

Karin Labarai Masu Alaka

Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa Afrika
NYSC – Sai An Gabatar Da Takardar NERD Kafin Shiga Bautar Ƙasa Afrika
Babban Malamin Musulunci Sheikh Usman Kusfa Zaria Ya Rasu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Kungiyar Miyetti Allah Ta Bukaci Mambobinta Su Marawa Dr. Jamilu Isiyaku Gwamna Baya A Gombe Afrika
Rundunar ‘Yan Sandan Kebbi Ta Dakile Yunkurin Garkuwa Da Mutune, Ta Kama Masu Laifi Afrika
Gidauniyar Jalo Wali Ta Ƙaddamar Da Bada Audugar Mata A Gombe Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Gobara Ta Lalata Shaguna Da Gidajen Abinci A Gombe Labarai
  • Kungiyar ‘Yan Jarida Ta Najeriya Ta Tabbatar Da Kyautata Rayuwar Mambobin ta Labarai
  • Eberechi Eze Ba Zai Buga Wasannin Da Ingila Za Tayiba Arteta Wasanni
  • Shugaban Kasar Iran Yace Kasar Bata Da Kiyayya Tsakaninta Da Amurkawa Afrika
  • Gwamna Inuwa Yahaya ya Rusa Majalisar Zantaswa ta Jihar Gombe Labarai
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed Afrika
  • Hare Hare A Kasar Congo Ya Jikkata Mutane Da Dama Afrika
  • Hamas Ta Mika Ma Isra’ila Gawar Daya Daga Cikin Mutane Biyu Sauran Duniya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.