Hukumar Bada agaji ta jihar Gombe wato SEMA da haɗin guiwar Hukumar Bada agajin Gaggawa ta Najeriya wato NEMA da Hukuma wayar da Kan al’umma ta kasar wato NOA ne suka Ziyarci Garin Dukku a jihar Gombe dake Najeriya domin fadakar da al’umma wanda taron ya gudana a sakatariyar Karamar Hukumar.

A jawabinsa Darakta a hukumar Bada agajin Gaggawa ta jihar Gombe Malam Ibrahim Nalado, ya bayyana cewa akwai Hasashen Samun ambaliyar Ruwan Sama a Sassan ƙasar ciki harda jihar Gombe da wassu kananan Hukumomin jihar.
Nalado ya Jadda da cewa, yana da kyau hukumomin su fadakar dasauran al’ummar da Sarakunan gargajiya Domin sakon ya je Wajen al’umma.

Itama anata gudunmawa Daraktan Hukumar wayar da Kan al’umma a jihar Gombe, Hajiya Maimuna Abubakar ta bayyana Farin cikinta yadda al’ummar Dukku Suka Karbi wannan Sako kana ta bukaci hadakai Domin tinkarar wannan matsala da Ake Hasashen faruwanta.

Anasu gudunmawa Kabiru Idris Molki na Hukumar Bada agajin Gaggawa ta kasar da Injiniya Dahiru Ajiya na Hukumar Bada agaji ta jiha sun zayyano Matsalolin da ake shiga Sakamakon ambaliyar tare da kawo Hanyoyin Kariya Domin Samun tsira.

Sunce Sakamakon taro a Abuja da wakilen jihohin Kasar nan inda aka bayyana Hasashen da zai’iya faruwa yasa gwamnatin jihar Gombe ta Bada umarnin zagayawa Domin fadakar da al’umma Domin Samun kariya.
Anasa Bangaren Mai Lura da Karamar Hukumar Dukku Wanda yasamu wakilincin Shugaban Sashin ESD Malam Ibrahim Muhammad ya bayyana godiyarsa Bisa wannan ziyarar fadakarwa Daga Hukumomin.
Mai Lura da Karamar Hukumar ya Jadda Aniyar goyon bayan Karamar Hukumar Dukku Wajen Samun nasarar wannan Gangamin Domin Taimakon al’ummar jihar Gombe, Arewa Maso Gabas Dama Najeriya Baki Daya.


