Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Masu Luwadi Na Fuskantar Tara Da Daurin Shekaru 20 A Nijar Afrika
  • Sakon Shugaban Kasar Najeriya Bola Ahmed Tinubu A Ranar Dimokraɗiyya Ta 2026 Afrika
  • Uefa Ta Zabi Artan, Ya Jagoranci Wasan Cin Kofin Uefa Super Cup Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Shugaba Tinubu Ya Kafa Kwamitin Gaggawa Akan Cutar Ebola Afrika
  • ‘Yan Sandan Gombe Sun Fara Kama Motocin Da Ba Su Da Lambar Rajista ko Masu Boye Lambobinsu Afrika

Hukumomin Bada Agaji Sun Fadakar Da Al’ummar Jihar Gombe
Published: May 15, 2026 at 6:59 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Hukumar Bada agaji ta jihar Gombe wato SEMA da haɗin guiwar Hukumar Bada agajin Gaggawa ta Najeriya wato NEMA da Hukuma wayar da Kan al’umma ta kasar wato NOA  ne suka Ziyarci Garin Dukku a jihar Gombe dake Najeriya domin fadakar da al’umma wanda taron ya gudana a sakatariyar Karamar Hukumar.

A jawabinsa Darakta a hukumar Bada agajin Gaggawa ta jihar Gombe Malam Ibrahim Nalado, ya bayyana cewa akwai Hasashen Samun ambaliyar Ruwan Sama a Sassan ƙasar ciki harda jihar Gombe da wassu kananan Hukumomin jihar.

Nalado ya Jadda da cewa, yana da kyau hukumomin su fadakar dasauran al’ummar da Sarakunan gargajiya Domin sakon ya je Wajen al’umma.

Itama anata gudunmawa Daraktan Hukumar wayar da Kan al’umma a jihar Gombe, Hajiya Maimuna Abubakar ta bayyana Farin cikinta yadda al’ummar Dukku Suka Karbi wannan Sako kana ta bukaci hadakai Domin tinkarar wannan matsala da Ake Hasashen faruwanta.

Anasu gudunmawa Kabiru Idris Molki na Hukumar Bada agajin Gaggawa ta kasar da Injiniya Dahiru Ajiya na Hukumar Bada agaji ta jiha sun zayyano Matsalolin da ake shiga Sakamakon ambaliyar tare da kawo Hanyoyin Kariya Domin Samun tsira.

Sunce Sakamakon taro a Abuja da wakilen jihohin Kasar nan inda aka bayyana Hasashen da zai’iya faruwa yasa gwamnatin jihar Gombe ta Bada umarnin zagayawa Domin fadakar da al’umma Domin Samun kariya.

Anasa Bangaren Mai Lura da Karamar Hukumar Dukku Wanda yasamu wakilincin  Shugaban Sashin ESD Malam Ibrahim Muhammad ya bayyana godiyarsa Bisa wannan ziyarar fadakarwa Daga Hukumomin.

Mai Lura da Karamar Hukumar ya Jadda Aniyar goyon bayan Karamar Hukumar Dukku Wajen Samun nasarar wannan Gangamin Domin Taimakon al’ummar jihar Gombe, Arewa Maso Gabas Dama Najeriya Baki Daya.

Afrika, Kiwon Lafiya, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya

Post navigation

Previous Post: Ana Cigaba Da Shirye-Shiryen Fara Gasar Kwallon Sarakuna A Gombe
Next Post: Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe

Karin Labarai Masu Alaka

Kungiyar Kwadago Ta Shirya Zanga-Zanga A Najeriya Najeriya
Dalibin Jami’a Ya Rasa Ransa A Birnin Dakar Yayin Zanga Zanga Afrika
Kasar Colombia Tare Da Amurka Zasu Fitar Da Man Venezuela Labarai
An Kamallah Jigilar Alhazain Najeriya Domin Hajjin 2026 Afrika
CAN: Da Alamu Daliban St. Mery Na Cikin Koshin Lafiya Najeriya
An Canza Shugabannin Hukumar Hakar Ma’adanai A Congo Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Masu Luwadi Na Fuskantar Tara Da Daurin Shekaru 20 A Nijar
  • Sakon Shugaban Kasar Najeriya Bola Ahmed Tinubu A Ranar Dimokraɗiyya Ta 2026
  • Za’a Bude Gasar Cin Kofin Kwallon Kafa Ta Duniya 2026
  • Uefa Ta Zabi Artan, Ya Jagoranci Wasan Cin Kofin Uefa Super Cup
  • Shugaba Tinubu Ya Kafa Kwamitin Gaggawa Akan Cutar Ebola

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • An Bude Makarantu A Najeriya Najeriya
  • An Kashe Mutane 25 Yayin Kai Wasu Hare Hare Jihar Adamawa Labarai
  • ‘Yan Daba Sunkai Hari Kasuwar Waya A Kano Afrika
  • Shirin Dare 2030 UTC Yau Laraba 11.19.2025 Rediyo
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai Afrika
  • Bana Ba Harka Ga ‘Yan-Wasan Kwallon Kafar Najeriya Wasanni
  • Hukumar DSS Ta Sake Kama Abubakar Malami Labarai
  • Liverpool Tayi Rashin Nasara A Wasanni Tara Wasanni
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.