Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u Afrika
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa Afrika
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa Afrika
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed Afrika

Ana Cigaba Da Shirye-Shiryen Fara Gasar Kwallon Sarakuna A Gombe
Published: May 13, 2026 at 12:58 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

An gudanar da bikin fitar da jadawalin wasannin Kofin Sarakunan jihar Gombe na shekarar 2026 cikin nasara a Cibiyar NITDA ICT da ke Jami’ar jihar Gombe, inda ya samu halartar sarakunan gargajiya, masu ruwa da tsaki a harkar kwallon kafa, ‘yan jarida da sauran baki daga sassa daban-daban na jihar Gombe

An shirya tare da daukar nauyin gasar ne daga GWG Sports. A yayin taron, an gabatar da sakonnin taya murna da fatan alheri daga masu ruwa da tsaki, sannan aka bayyana jadawalin wasannin kungiyoyin masarautu da na gargajiya da za su fafata a gasar.

Da yake jawabi a wajen taron, Shugaban Kwamitin Shirye-shiryen gasar Ahmad Shuaibu Gara Gombe, ya yaba wa sarakunan gargajiya da kafafen yada labarai bisa ci gaba da bayar da gudunmawa wajen bunkasa gasar. Ya ce masarautun jihar Gombe na da matukar rawar da suke takawa wajen samar da hazikan ‘yan wasan kwallon kafa da ke taimakawa ci gaban wasanni a jihar da ma kasa baki daya.

Ya kara da cewa an kirkiri wannan gasa ne domin karfafa hadin kai, inganta shigar matasa cikin harkar wasanni, da kuma gano sabbin basira a fadin jihar. Ya bayyana cewa an takaita shiga gasar ga kungiyoyin da aka yi rajista na masarautu da chiefdoms.

An gudanar da fitar da jadawalin karkashin jagorancin Shugaban Kwamitin Fasaha, Alhaji Abdulkadir Kawu, tare da Daraktan gasar, Haruna Isa Kalshingi, inda kungiyoyi suka zabi cibiyoyin wasannin su da suka hada da Kananan Hukumomin Funakaye, Deba da Billiri.

Haka kuma, taron ya samu halartar wakilan masarautu, jami’an kula da harkar kwallon kafa, da sauran masu ruwa da tsaki, wadanda suka yaba da cigaban gasar a matsayin wata hanya ta inganta zaman lafiya, hadin kai da bunkasa matasa ta hanyar wasanni.

An kammala taron ne da bayyana jadawalin wasanni a hukumance, addu’ar rufewa, da kuma daukar hoton tunawa tare da mahalarta daga masarautu da chiefdoms goma sha biyu na jihar Gombe

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Shirye-Shirye

Post navigation

Previous Post: Gwamnatin Najeriya Zata Samar Da Sabbin Dakunan Karatun Dalibai
Next Post: Hukumomin Bada Agaji Sun Fadakar Da Al’ummar Jihar Gombe

Karin Labarai Masu Alaka

Kamfanin Hakar Ma’adanai Na Kasar Kanada Ya Cigaban Da Aikinsa Labarai
Kasar India Ta Sayi Iskar Gas Daga Iran Labarai
Azumin Ramadan Yahadu Da Azumin Lent Da Mabiya Addinin Kirista Sukeyi A Wannan Shekarar Labarai
Amurka Tace Zata Gama Yakin Iran Cikin Makonni Afrika
INEC Mayar Da Lokacin Zaɓen 2027 Kafin Azumi Najeriya
Na Duke Tsohon Ciniki Shirye-Shirye

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Shugaba Tinubu Ya Kara Aika Sunayen Jakadu Ga Majalisa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Kotun Uganda Tayi Watsi Da Karar Hukumomin Kasar Afrika
  • Trump Yayi Kira Ga ‘Yan Ƙasar Iran Su Ci Gaba Da Zanga Zanga Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamna Fubara: Rashin Kariya daga PDP Ne Ya Tilasta Ni Komawa APC Siyasa
  • Akwai Bukatar Nazari Game Da Dangantakar Iran Da Kasashen Gulf Amurka
  • Barayin Waya Sun Yanke Yatsun Hannu Guda Biyu Da Gefen Kunne A Bauchi Labarai
  • Karo Na Biyu Cikin Kwanaki 29 An Samu Gobara A Kasuwar Katako Labarai
  • Shugaban Kasar Najeriya Ya Nada Sabon Ministan Kudi Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.