Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Masu Luwadi Na Fuskantar Tara Da Daurin Shekaru 20 A Nijar Afrika
  • Sakon Shugaban Kasar Najeriya Bola Ahmed Tinubu A Ranar Dimokraɗiyya Ta 2026 Afrika
  • Uefa Ta Zabi Artan, Ya Jagoranci Wasan Cin Kofin Uefa Super Cup Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Shugaba Tinubu Ya Kafa Kwamitin Gaggawa Akan Cutar Ebola Afrika
  • ‘Yan Sandan Gombe Sun Fara Kama Motocin Da Ba Su Da Lambar Rajista ko Masu Boye Lambobinsu Afrika

Ana Cigaba Da Shirye-Shiryen Fara Gasar Kwallon Sarakuna A Gombe
Published: May 13, 2026 at 12:58 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

An gudanar da bikin fitar da jadawalin wasannin Kofin Sarakunan jihar Gombe na shekarar 2026 cikin nasara a Cibiyar NITDA ICT da ke Jami’ar jihar Gombe, inda ya samu halartar sarakunan gargajiya, masu ruwa da tsaki a harkar kwallon kafa, ‘yan jarida da sauran baki daga sassa daban-daban na jihar Gombe

An shirya tare da daukar nauyin gasar ne daga GWG Sports. A yayin taron, an gabatar da sakonnin taya murna da fatan alheri daga masu ruwa da tsaki, sannan aka bayyana jadawalin wasannin kungiyoyin masarautu da na gargajiya da za su fafata a gasar.

Da yake jawabi a wajen taron, Shugaban Kwamitin Shirye-shiryen gasar Ahmad Shuaibu Gara Gombe, ya yaba wa sarakunan gargajiya da kafafen yada labarai bisa ci gaba da bayar da gudunmawa wajen bunkasa gasar. Ya ce masarautun jihar Gombe na da matukar rawar da suke takawa wajen samar da hazikan ‘yan wasan kwallon kafa da ke taimakawa ci gaban wasanni a jihar da ma kasa baki daya.

Ya kara da cewa an kirkiri wannan gasa ne domin karfafa hadin kai, inganta shigar matasa cikin harkar wasanni, da kuma gano sabbin basira a fadin jihar. Ya bayyana cewa an takaita shiga gasar ga kungiyoyin da aka yi rajista na masarautu da chiefdoms.

An gudanar da fitar da jadawalin karkashin jagorancin Shugaban Kwamitin Fasaha, Alhaji Abdulkadir Kawu, tare da Daraktan gasar, Haruna Isa Kalshingi, inda kungiyoyi suka zabi cibiyoyin wasannin su da suka hada da Kananan Hukumomin Funakaye, Deba da Billiri.

Haka kuma, taron ya samu halartar wakilan masarautu, jami’an kula da harkar kwallon kafa, da sauran masu ruwa da tsaki, wadanda suka yaba da cigaban gasar a matsayin wata hanya ta inganta zaman lafiya, hadin kai da bunkasa matasa ta hanyar wasanni.

An kammala taron ne da bayyana jadawalin wasanni a hukumance, addu’ar rufewa, da kuma daukar hoton tunawa tare da mahalarta daga masarautu da chiefdoms goma sha biyu na jihar Gombe

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Shirye-Shirye

Post navigation

Previous Post: Gwamnatin Najeriya Zata Samar Da Sabbin Dakunan Karatun Dalibai
Next Post: Hukumomin Bada Agaji Sun Fadakar Da Al’ummar Jihar Gombe

Karin Labarai Masu Alaka

Harin Isra’ila A Gaza Da Jirgi Maras Matuki Ya Kashe Mutane Afrika
Kasar Habasha Ta Cimma Matsaya Da Masu Binta Bashi Afrika
Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Hamma Saleh Ya Yi Fatali da Bai Wa Pantami Takarar Gwamna a PDP Afrika
EFCC Ta Cafke Fitacciyar Jarumar Kannywood Samha Inuwa Labarai
Shugaban Libya Ya Sayi Jirage Marasa Matuka Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Masu Luwadi Na Fuskantar Tara Da Daurin Shekaru 20 A Nijar
  • Sakon Shugaban Kasar Najeriya Bola Ahmed Tinubu A Ranar Dimokraɗiyya Ta 2026
  • Za’a Bude Gasar Cin Kofin Kwallon Kafa Ta Duniya 2026
  • Uefa Ta Zabi Artan, Ya Jagoranci Wasan Cin Kofin Uefa Super Cup
  • Shugaba Tinubu Ya Kafa Kwamitin Gaggawa Akan Cutar Ebola

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Gobara Ta Tashi A Hukumar FIRS Dake Abuja Najeriya
  • Hamma Saleh Ya Yi Fatali da Bai Wa Pantami Takarar Gwamna a PDP Afrika
  • Mawakiyar Amurka Cardi B. Ta Cashe A Saudi Araibiya Nishadi
  • Za A Rantsar Da Mainasara Kogo A Matsayin Shugaban Kundin Da’ar Ma’aikata Labarai
  • Kasashen Duniya Sunyi Tir Da Hambarar Da Gwamnatin Venezuela Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • FIFA, Ta Raba Jaddawalin Rukuni Na Gasar Kofin Duniya 2026. Wasanni
  • Gwamnan Jihar Filato Ya Karbi Katin APC Labarai
  • An tura tsohon ministan Ilimin Nijar gidan yari saboda zargin aikata fyade ga wata daliba. Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.