Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

Kasashen Cambvodia Da Thailand Sun Kulla Yarjejeniyar Tsagaita Wuta
Published: December 13, 2025 at 9:30 AM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: December 13, 2025

Cambvodia ta ce sojoji da jiragen yakin kasar thailand suna ci gaba da kai hare-hare a wasu yankunan bakin iyakarsu a ranar asabar da safe, sa’o’i bayan da shugaba Donald Trump na Amurka yayi ikirarin cewa ya kulla yarjejeniyar tsagaita wuta a tsakanin makwabtan biyu.

Ma’aikatar yada labarai ta Cambodia ta ce sojojin Thailand ba su daina kai hare-haren kan cibiyoyin Cambodia ba.

Rundunar sojojin Thailand ta mayarda martani da cewa Cambodia tana ci gaba da keta dokoki na kasa da kasa ta hanyar auna hare-hare a kan cibiyoyin fararen hula tare da dasa nakiyoyi.

Shugaba Trump yace Thailand da Cambodia sun yarda zasu tsagaita bude wuta daga jiya jumma’a a bayan tattaunawar da yayi ta wayar tarho da firayim ministan Thailand Anutuin Charnvirakul da firimiyan Cambodia Hun Manet.

Sai dai kuma babu daya daga cikinsu da yayi maganar cewa an cimma wata yarjejeniya a bayanan da suka yi bayan tattaunawa da shugaban na Amurka, har ma firayim ministan Thailand din yace babu wata tsagaita wutar da aka cimma.

A cikin wata sanarwar da ya fitar ranar asabar a shafin Facebook, firimiyan Cambodia Manet yayi nuni da wayar da suka yi da shugaba trump da tattaunawar da suka yi tun da fari da firayim ministan Malaysia Anwar Ibrahim, yana mai fadin cewa kasarsa tana ci gaba da neman hanyar warware rikicin bakin iyakar cikin lumana.

Tsaro

Post navigation

Previous Post: Makarantun Allo Zasu Yi Gogayya Da Na Boko
Next Post: Amurka Ta Daina Bawa Israila Bayanan Sirri

Karin Labarai Masu Alaka

Shugaba Trump Ya Bukaci A Cigaba Da Zanga Zanga A Iran Labarai
Isra’ila Ta Zantar Da Hukuncin Kisa Ga Masu Kai Hare Hare Labarai
Wasu Mutane 15 Sun Rasa Rayukan Su A Gabashin Kwango Afrika
Shugabannin Kasar Australia Sun Bukaci ‘Yan Kasar Suyi Zanga Zanga Cikin Lumana Afrika
Dakaru Sun Hallaka ’Yan Ta’adda Masu Yawa – DHQ Afrika
An Gudanar Da Addu’o’i Na Musamman Game Da Matsalar Tsaro A Najeriya Najeriya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Ana Zargin Cewa ‘Yan Bindiga Biyun Nan Mambobin Kungiyar ISIS Ne Amurka
  • Shirin Safe 0500 UTC Yau Juma’a 11.21.2025 Rediyo
  • Amurka Tayi Barazanar Rage Tallafinta Wa Sudan Ta Kudu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Jirgi Marar Matuka Yayi Luguden Wutan A Abu Dhabi Afrika
  • Shugaba Tinubu Ya Tafi Kasar Faransa Afrika
  • Za’a Saka Tarihin Trump A Manhajar Makarantu Don Jajircewasa Da Kwazo Amurka
  • Hamas Ta Mika Ma Isra’ila Gawar Daya Daga Cikin Mutane Biyu Sauran Duniya
  • Tinubu: Zamu Kara Kyautata Samar Da Kayan Aiki Ga Jami’an Tsaro Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.