Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Kasashen Cambvodia Da Thailand Sun Kulla Yarjejeniyar Tsagaita Wuta
Published: December 13, 2025 at 9:30 AM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: December 13, 2025

Cambvodia ta ce sojoji da jiragen yakin kasar thailand suna ci gaba da kai hare-hare a wasu yankunan bakin iyakarsu a ranar asabar da safe, sa’o’i bayan da shugaba Donald Trump na Amurka yayi ikirarin cewa ya kulla yarjejeniyar tsagaita wuta a tsakanin makwabtan biyu.

Ma’aikatar yada labarai ta Cambodia ta ce sojojin Thailand ba su daina kai hare-haren kan cibiyoyin Cambodia ba.

Rundunar sojojin Thailand ta mayarda martani da cewa Cambodia tana ci gaba da keta dokoki na kasa da kasa ta hanyar auna hare-hare a kan cibiyoyin fararen hula tare da dasa nakiyoyi.

Shugaba Trump yace Thailand da Cambodia sun yarda zasu tsagaita bude wuta daga jiya jumma’a a bayan tattaunawar da yayi ta wayar tarho da firayim ministan Thailand Anutuin Charnvirakul da firimiyan Cambodia Hun Manet.

Sai dai kuma babu daya daga cikinsu da yayi maganar cewa an cimma wata yarjejeniya a bayanan da suka yi bayan tattaunawa da shugaban na Amurka, har ma firayim ministan Thailand din yace babu wata tsagaita wutar da aka cimma.

A cikin wata sanarwar da ya fitar ranar asabar a shafin Facebook, firimiyan Cambodia Manet yayi nuni da wayar da suka yi da shugaba trump da tattaunawar da suka yi tun da fari da firayim ministan Malaysia Anwar Ibrahim, yana mai fadin cewa kasarsa tana ci gaba da neman hanyar warware rikicin bakin iyakar cikin lumana.

Tsaro

Post navigation

Previous Post: Makarantun Allo Zasu Yi Gogayya Da Na Boko
Next Post: Amurka Ta Daina Bawa Israila Bayanan Sirri

Karin Labarai Masu Alaka

‘Yan Tawayen Kasar Kwango Ne Suka Kai Hari Filin Jirgin Saman Kisangani Labarai
Iran Zata Mayarwa Amurka Martani Amurka
Harin Jirgi Maras Matuki Ya Hallaka Mutane A Sudan Labarai
An Kashe Falatsinawa Biyar A Wani Hari Da Isra’ila Takai Wata Makaranta A Gaza Tsaro
Babu Alamar Tsagaita Wuta A Yaki Da Akeyi Tsakanin Isra’ila Da Amurka Afrika
Dakarun Sakai A Kasar Sudan Sun Kashe Mutane 28 A Wani Farmaki Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Yakin Gabas Ta Tsakiya Ya Kawo Cikas Ga Cinikin Nama A Kenya
  • Sabon Jagoran Addinin Iran Mojtaba Khameni Yaji Rauni Kuma Ya Nakasa
  • Shugaba Trump Yace Amurka Takai Hari Kharg Tsibiri a Kasar Iran
  • MDD: Fiye Da Farar Hula Metan 200 Suka Mutu A Sudan
  • Jami’ai A Afirka Sunce Tashin Farashin Mai Kalubale Ne Ga Tattalin Arziki

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Jihar Gombe Ta Saka Hannu Kan Yarjejeniya Da Kamfanonin Tunisiya Kimiya
  • AFCON 2025, Jerin Abubuwan Da Aka Haramta Wa Magoya Baya Wasanni
  • Najeriya Da Kasar Saudiya Sun Kulla Yarjejeniyar Tsaro Labarai
  • Wani Ya Yiwa ‘Yar Sa Mai Shekaru 8 Fyade A Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Fiye Da Mutane Miliyan Hudu Suna Fuskantar Barazanar Yunwa A Somaliya Sauran Duniya
  • Kasashe 5 Da Ke Fama Da Matsanancin Zazzabin Cizon Sauro Rediyo
  • Ronaldo Da Messi Ka Iya Hadu A Gasar Cin Kofin Duniya: Ta Ya Ya ? Wasanni
  • PDP Zata Karbi Mulki 2027 Inji Shugabannin Jam’iyar Siyasa
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.