Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • PDP Ta Tsayar da Goodluck Jonathan Takarar Shugaban Kasa Afrika
  • Hawan Gidan Gwamnati A Jihar Gombe Afrika
  • Hawan Babbar Sallah A Masarautar Kaltungo Dake Jihar Gombe Afrika
  • Sarkin Gombe Ya Yabi Nasarorin Inuwa Yahaya A Fannonin Tsaro Da Raya Kasa Afrika
  • Tinubu Ya Jaddada Aniyar Rage Tsadar Rayuwa Da Samar da Ayyukan Yi Afrika

Jirgin Ruwa Ya Kife A Yammacin Kasar Gambiya
Published: January 2, 2026 at 12:00 PM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: January 2, 2026

Kasar Gambia ta ceto mutane 96, da gawarwakin wasu mutane bakwai, bayan jirgin ruwa dauke da fiye da bakin haure 200 ya kife a yammacin kasar, kamar yadda ma’aikatar tsaron Gambia ta fada a cikin wata sanarwa data bayar ranar Alhamis. Ma’aikatar ta kara da cewa ana ci gaba da aikin ceto.

Wannan shine mummunar hatsari na baya bayan nan akan hanya mafi hadari da bakin haure galibi daga Afirka ta yamma suke bi a kokarin da suke yi na isa Spain ko Andalusiya ta wani tsibiri da ake kira Canary Island.

An sami rahoton cewa jirgin ya kife ne a tsakiyar dare kusa da wani kauye daga bisani aka sami jirgin ya kafe cikin yashi a wani yanki na kasar dake arewaci, kamar yadda ma’aikatar tsaron kasar ta fada.

Kungiyar tarayyar turai tace bakin haure na ba safai ba dubu 46 ne suka isa tsibirin Canary a shekarar 2024, adadi mafi yawa da aka gani, fiye da mutane dubu 10 suka mutu a kokarin su na zuwa turai, wanda ya nuna karin kashi 58 cikin dari idan aka kwatanta da shekarar 2023, inji wata kungiyar kare hakkin bil’adma da ake kira Caminando.

Amma alkaluma daga hukumar kula da shige da fice ta kunigyar tarayyar turai watau EU a takaice, tace a watanni 11 na shekarar 2025, an sami ragowar korarar irin wadanan mutanen daga Afirka ta yamma masu niyyar zuwa turai da kashi 60 cikin dari.

Hukumar shige da fice ta turai tace raguwar masu tafiya turan, ya ta’allaka ne kan matakan hana tafiye tafiye masu tsanani da kasashe da ake tashi cikinsu wadanda suke aiki da kungiyar tarayar turan suke dauka.

Akalla mutane 70 ne suka halaka cikin watan Agustan bara, lokacin da jirgin da suke ciki, da aka ce ya ta so daga Gambiya ya kife, a hatsari mafi muni da aka gani a cikin shekarun baya bayan nan.

Labarai

Post navigation

Previous Post: Jamhuriyar Congo Zata Cigaba Da Fitar Da Ma’adanai
Next Post: Darajar Kudin Afirka Ta Kudu Ya Tashi

Karin Labarai Masu Alaka

PDP Ta Tsayar da Goodluck Jonathan Takarar Shugaban Kasa Afrika
Hukumar Zabe Ta Saukaka Gudanar Da Rijistar Katin Zabe A Najeriya Labarai
Kasashen Yankin Gulf Sun Bukaci Amurka Takawo Karshen Iran Afrika
Amurka Da Tarayyar Turai Sun Fidda Sanarwa Afrika
Hukumar DSS Ta Sake Kama Abubakar Malami Labarai
Gwamnatin Tinubu Zata Gyara Hanyar Akwanga Zuwa Jos Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • PDP Ta Tsayar da Goodluck Jonathan Takarar Shugaban Kasa
  • Hawan Gidan Gwamnati A Jihar Gombe
  • Hawan Babbar Sallah A Masarautar Kaltungo Dake Jihar Gombe
  • Sarkin Gombe Ya Yabi Nasarorin Inuwa Yahaya A Fannonin Tsaro Da Raya Kasa
  • Tinubu Ya Jaddada Aniyar Rage Tsadar Rayuwa Da Samar da Ayyukan Yi

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Shirin Safe 0500 UTC Yau Asabar 11.22.2025 Rediyo
  • Gwamnan Neja Bago Na Cin Zarafin Talakawan Da Suka Zabe Shi Labarai
  • Gwamnatin Kano Zata Dauki Mataki Game Da Kisan Dorayi Tsaro
  • Kungiyoyin Mata A Jihar Filato Sunyi Gangamin Samun Jagorancin Siyasa Afrika
  • Isra’ila Zata Rusa Gidajen Da Suke Iyakarta Da Lebanon Labarai
  • Aliko Dangote: Faruk Ahmed Ya Ci Amanar ‘Yan Najeriya! Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Iran Ta Karyata Tattaunawa Da Washington Afrika
  • Za’a Fuskanci Bala’in Yunwa A Najeriya Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.