Kasar Gambia ta ceto mutane 96, da gawarwakin wasu mutane bakwai, bayan jirgin ruwa dauke da fiye da bakin haure 200 ya kife a yammacin kasar, kamar yadda ma’aikatar tsaron Gambia ta fada a cikin wata sanarwa data bayar ranar Alhamis. Ma’aikatar ta kara da cewa ana ci gaba da aikin ceto.

Wannan shine mummunar hatsari na baya bayan nan akan hanya mafi hadari da bakin haure galibi daga Afirka ta yamma suke bi a kokarin da suke yi na isa Spain ko Andalusiya ta wani tsibiri da ake kira Canary Island.
An sami rahoton cewa jirgin ya kife ne a tsakiyar dare kusa da wani kauye daga bisani aka sami jirgin ya kafe cikin yashi a wani yanki na kasar dake arewaci, kamar yadda ma’aikatar tsaron kasar ta fada.
Kungiyar tarayyar turai tace bakin haure na ba safai ba dubu 46 ne suka isa tsibirin Canary a shekarar 2024, adadi mafi yawa da aka gani, fiye da mutane dubu 10 suka mutu a kokarin su na zuwa turai, wanda ya nuna karin kashi 58 cikin dari idan aka kwatanta da shekarar 2023, inji wata kungiyar kare hakkin bil’adma da ake kira Caminando.
Amma alkaluma daga hukumar kula da shige da fice ta kunigyar tarayyar turai watau EU a takaice, tace a watanni 11 na shekarar 2025, an sami ragowar korarar irin wadanan mutanen daga Afirka ta yamma masu niyyar zuwa turai da kashi 60 cikin dari.
Hukumar shige da fice ta turai tace raguwar masu tafiya turan, ya ta’allaka ne kan matakan hana tafiye tafiye masu tsanani da kasashe da ake tashi cikinsu wadanda suke aiki da kungiyar tarayar turan suke dauka.
Akalla mutane 70 ne suka halaka cikin watan Agustan bara, lokacin da jirgin da suke ciki, da aka ce ya ta so daga Gambiya ya kife, a hatsari mafi muni da aka gani a cikin shekarun baya bayan nan.


