Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Jirgin Ruwa Ya Kife A Yammacin Kasar Gambiya
Published: January 2, 2026 at 12:00 PM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: January 2, 2026

Kasar Gambia ta ceto mutane 96, da gawarwakin wasu mutane bakwai, bayan jirgin ruwa dauke da fiye da bakin haure 200 ya kife a yammacin kasar, kamar yadda ma’aikatar tsaron Gambia ta fada a cikin wata sanarwa data bayar ranar Alhamis. Ma’aikatar ta kara da cewa ana ci gaba da aikin ceto.

Wannan shine mummunar hatsari na baya bayan nan akan hanya mafi hadari da bakin haure galibi daga Afirka ta yamma suke bi a kokarin da suke yi na isa Spain ko Andalusiya ta wani tsibiri da ake kira Canary Island.

An sami rahoton cewa jirgin ya kife ne a tsakiyar dare kusa da wani kauye daga bisani aka sami jirgin ya kafe cikin yashi a wani yanki na kasar dake arewaci, kamar yadda ma’aikatar tsaron kasar ta fada.

Kungiyar tarayyar turai tace bakin haure na ba safai ba dubu 46 ne suka isa tsibirin Canary a shekarar 2024, adadi mafi yawa da aka gani, fiye da mutane dubu 10 suka mutu a kokarin su na zuwa turai, wanda ya nuna karin kashi 58 cikin dari idan aka kwatanta da shekarar 2023, inji wata kungiyar kare hakkin bil’adma da ake kira Caminando.

Amma alkaluma daga hukumar kula da shige da fice ta kunigyar tarayyar turai watau EU a takaice, tace a watanni 11 na shekarar 2025, an sami ragowar korarar irin wadanan mutanen daga Afirka ta yamma masu niyyar zuwa turai da kashi 60 cikin dari.

Hukumar shige da fice ta turai tace raguwar masu tafiya turan, ya ta’allaka ne kan matakan hana tafiye tafiye masu tsanani da kasashe da ake tashi cikinsu wadanda suke aiki da kungiyar tarayar turan suke dauka.

Akalla mutane 70 ne suka halaka cikin watan Agustan bara, lokacin da jirgin da suke ciki, da aka ce ya ta so daga Gambiya ya kife, a hatsari mafi muni da aka gani a cikin shekarun baya bayan nan.

Labarai

Post navigation

Previous Post: Jamhuriyar Congo Zata Cigaba Da Fitar Da Ma’adanai
Next Post: Darajar Kudin Afirka Ta Kudu Ya Tashi

Karin Labarai Masu Alaka

Fintiri: Zamu Maida Jihar Adamawa Sabuwar Duniya Labarai
Masar Tayi Yarjejeniyar Makamashi Da Kasashen Norway Da China Labarai
‘Yan Bindiga Sun Kashe Dan Gaddafi A Gidansa Dake Kasar Libya Afrika
An Kama Tsohon Jakadan Birtaniya A Amurka Peter Mandelson Amurka
Shugaban Kasar Afirka Ta Tsakiya Ya Roki Rasha Ta Taimakawa Kasar Afrika
Anfara Samun Sakamakon Wucin Gadi a Kasar Guinea Conakry Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Harin Iran A Kasar Saudiya Ya Haifar Da Tattaunawa Tsakanin Shugabanni
  • An Kaiwa Sojojin Ghana Hari Da Makami Mai Linzami
  • Kasar Ghana Zata Sauya Inda Take Kai Sarrafa Gwal
  • ‘Yan Bindiga Sun Hallaka Sojoji 15 Da Wasu Fararen Hula A Benin
  • Hukumomi A Kasar Syri Lanka Suna Kokarin Fidda Jirgin Yakin Iran Daga Kasar

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Afirka Ta Kudu Ta Kubutar Da ‘Yan Kasar Da Suke Taya Sojojin Rasha Yaki Afrika
  • Magoya Bayan Dan Hamayya A Afirka Ta Kudu Sun Hallara A Kotu Afrika
  • Farashin Mai Ya Fadi Fiye Da Dala Daya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ana Cigaba Da Samun Hare Hare Da Jiragen Marasa Matuki A Sudan Labarai
  • CBN: An Samu Ƙaruwar Masu Cin Bashin Banki Basa Biya Najeriya
  • Kamfanin NNPC Yana Tattaunawa Da Wani Kamfanin Kasar China Labarai
  • Gwamnatin Gombe: Babu Hannun mu a Cin Zarafin Kansilan Mazabar Shamaki Siyasa
  • Shirin Safe 0500 UTC Yau Alhamis 11.20.2025 Rediyo
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.