Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai Afrika
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari Afrika
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe Afrika
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS Afrika
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe Afrika

Anakan Bincike Wajen Gano Dan Bindigar Da Ya Kashe Dalibai Biyu A Jihar Rhode Island
Published: December 17, 2025 at 5:01 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Hukumomi a jihar Rhode Island a Amurka sun sake rokon jama’a ranar talata da su taimaka musu da wajen gano dan bindigar da ake zaton shine aka gan shi a wasu hotunan bidiyo, wanda kuma ake zargin shine ya bindige ya kashe wasu dalibai biyu na Jami’ar Brown a karshen mako.

A yayin da aka shige kwanaki uku ana farautar dan bindigar, kuma jama’a suna ci gaba da zaman dar-dar, jami’ai a birnin Providence na Rhode Island sun ce har yanzu ba su gane ko wanene dan bindigar ba.

Sun nuna wasu hotunan bidiyo da suka nuna mutumin yana kai gwauro da mari a kusa da inda aka yi harbin a ranar asabar, yana sanye da kaya masu duhu, kuma ya rufe fuskarsa da kyalle.

Baturen ‘yan sanda na birnin Providence, Oscar Perez, yace masu bincike suna fatan cewa wani wanda ya san mutumin zai iya gane shi ta hanyar ganin yadda yake tafiya da motsi da jikinsa.

Yace ‘yan sanda suna da shaidar cewa an ga wannan mutumin a wurin da misalin karfe 10.30 na safiyar asabar, fiye da awa biyar ke nan kafin a yi harbin.

Jami’ai suka ce suna da kwarin guiwar cewa mutumin da aka gani a wadannan hotunan bidiyo shine dan bindigar.

Amurka

Post navigation

Previous Post: Hukumar Ƴan Sanda Ta Musanta Zargin Kashe Ɗan Achaba a Gombe
Next Post: Ministan Kudin Najeriya: Bamu Samu Kudaden Da Muke Tsammani A Wannan Shekarar Ba

Karin Labarai Masu Alaka

Mayakan Houthi Zasu Shiga Yakin Amurka Da Isra’ila Afrika
Shugaba Trump Yace Amurka Takai Hari Kharg Tsibiri a Kasar Iran Afrika
Masu Kare Hakkin ‘Yan Gudun Hijira A Amurka Sun Mika Koke Amurka
Yaki Tsakanin Amurka, Isra’ila Da Iran Ya Shiga Kwana Na Biyar Afrika
Kasar Amurka Da Denmark Suna Rikici Akan Iyakar Greenland Amurka
Kasar Afirka Ta Kudu Ta Tsare Wasu Amurkawa Amurka

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Trump Da Bin Salman Da Wasu Kasashe Za Su Sa Hannu A Rikicin Sudan Labarai
  • Shugaban Amurka Yace Zayyi Wahala A Cimma Yarjejeniya Tsakanin Isra’ila, Amurka Da Iran Amurka
  • Jami’an Tsaro Suna Farautar Wasu ‘Yan Ta’adda A Najeriya Afrika
  • Shugaban Kasar Madagascar Ya Kori Prime Minista Da ‘Yan Majalisa Afrika
  • Okoye Na Shirin Maye Gurbin Nwabali, AFCON 2025: Wasanni
  • Jami’ai A Mexico Sun Tabbatar Da Kashe Shugaban Masu Shan Ƙwaya Nemesio Oseguera Labarai
  • Gobara Ta Tashi A Hukumar FIRS Dake Abuja Najeriya
  • Tsananta Hukunci Ga Masu Fyade Kan Takaita Cin Zarafin Yara Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.