Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

An Zargi Babban Mai Gabatar Da Kara A Kotun Duniya Ta ICC
Published: March 23, 2026 at 7:28 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Zarge-zargen aikata ba daidai ba na lalata da aka yi wa babban mai gabatar da ƙara na Kotun Hukunta Manyan Laifuka ta Duniya (ICC) na ci gaba da kasancewa ƙarƙashin nazari daga ɓangaren zartarwa na kotun, a cewar wata takardar cikin gida da aka rabawa ma’aikata jiya Lahadi, wadda kamfanin dillancin labarai na Reuters ya gani.

Babban mai gabatar da ƙara na ICC, Karim Khan, wanda ke binciken laifukan yaƙi, laifukan cin zarafin bil’adama da kuma kisan kare dangi, ya janye daga aikinsa na ɗan lokaci domin ba da dama ga bincike kan zargin cewa yana da wata alaƙar ta cin zarafin wata lauya a ofishinsa ba tare da amincewarta ba. Ya musanta aikata wani laifi.

Lauyoyin Khan sun bayyana a martanin su da suka bayar bayan Reuters ta wallafa rahotonta ranar Lahadi cewa ana sa ran hukumar tafiyar da ICC za ta gana a yau Litinin domin duba shawarwari da sakamakon da wani kwamiti na alkalai masu zaman kansu ya bayar, wanda har yanzu ba a bayyana shi ga jama’a ba.

“Alkalan sun gabatar da cikakken nazari mai zurfi tare da hujjoji, inda suka cimma matsaya gaba ɗaya cewa bayanan gaskiya da aka tattara ba su tabbatar da aikata ba daidai ba ko karya doka ba. Abin da ya rage yanzu shi ne shugabannin siyasa a cikin Hukumar gudanarwa su tabbatar da wannan kimantawa da Kwamitin ya yi,” in ji lauyoyin Khan a cikin wata sanarwar imel.

Afrika, Amurka, Labarai

Post navigation

Previous Post: Iran Zata Kai Hari Tashar Makamashin Ruwa A Gulf
Next Post: Akwai Yiwuwar Farashin Mai Zai Kara Tashi

Karin Labarai Masu Alaka

NITDA Da GOSIDEC Sun Horar Da Ma’aikatan Gombe Don Inganta Ayyukan Gwamnati Afrika
‘Yan Bindiga Sun Jikkata Mutane A Arewacin Kasar Benin Afrika
Shugaban Hukumar NAHCON Ya Yabawa ‘Yan Jarida Kiwon Lafiya
An Kaddamar Da Kwamitin Kwallon Kafa A Tsakanin Masarautun Jihar Gombe Labarai
Shugaban Majalisar Tarayyar Turai Yace Rasha Tana Cin Ribar Yakin Gabas Ta Tsakiya Afrika
Shugaba Trump Yayi Barazanar Tura Sojoji Ga Masu Zanga Zanga Amurka

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Amurka Na Shirin Kauracewa Taron Kungiyar Kasashen G20 Afrika
  • Amurka Ta Sanya Hanu Kan Yarjejeniyar Kiwon Lafiya Da Ƙasashen Madagascar, Saliyo, Botswana, Ethiopia Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ma’aikatan Tattara Kudin Haraji Sunyi Rikici Da Masu Babura A Bauchi Najeriya
  • Eberechi Eze Ba Zai Buga Wasannin Da Ingila Za Tayiba Arteta Wasanni
  • Mizanin Tattalin Arzikin Najeriya Na 2024 Ya Karu Da Kashi 3.84% Labarai
  • Abba Kabir: Zamu Samar da Jirage Marasa Matuka A Kano Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Togo Ta Kama Tsohon Shugaban Kasar Burkina Faso Saboda Kitsa Juyin Mulki Afrika
  • EFCC Ta Tsare Tsohon Minista Abubakar Malami Tsaro
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.