Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama Afrika
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara Afrika
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe Afrika
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro Afrika
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa Afrika

Amurka Na Shirin Kauracewa Taron Kungiyar Kasashen G20
Published: November 21, 2025 at 4:36 AM | By: Yusuf Aliyu Harande

Fadar shugaban Amurka ta White House ta musanta kalamun da shugaba Cyril Ramaphosa na Afrika Ta Kudu (ATK) yayi jiya Alhamis inda yake cewa Amurka tana tunanin canja ra’ayinta game da kauracewa taron kolin kasashen kungiyar G20 a birnin Johannesburg.

A wajen wani taron manema labarai da manyan jami’an Kungiyar Tarayyar Turai jiya alhamis, shugaba Ramaphosa yace sun samu wata sanarwa daga Amurka game da canja ra’ayi ko kuma dai halartar taron a wani matsayi.

Wata jami’ar White House ta musanta wannan, tana mai cewa karamin jakadan Amurka dake Pretoria zai je wurin taron ne domin karbar ragamar jagorancin kungiyar na karba-karba wanda zai komo hannun Amurka, amma ba wai don halartar wani abu na taron ba.

Gwamnatin shugaba Trump ta ce Amurka ba zata halarci taron farko na kungiyar G20 da za a yi a Afirka ba, tana mai zargin cewa ATK mai masaukin baki, wadda turawa ‘yan tsiraru na kasar suka mulke ta har zuwa 1994, tana gallazawa da cin mutuncin turawan kasar.

Ita dai kungiyar ta G20, kungiya ce ta kasashe 19 da suka kunshi wadanda suka fi arziki da kuma wadanda tattalin arzikinsu ke tasowa sosai. A shekarar 2023, KTT da KTA, sun shiga a zaman membobi masu wakiltar kasashensu, kungiyar ta zamo mai membobi 21.

Wannan kungiya, ba kamar kungiyar G7 ta kasashe mafiya arziki zalla ba, tana mayarda hankulanta ne kan tattalin arzikin duniya da ayyukan raya kasa. Sai dai kungiyar ba ta da hedkwata, kuma ba ta cimma shawarwarin da dole membobi suyi aiki da su, abinda ya sa masu sukar lamiri suke ce kungiyar haushi kawai ta iya, ba ta da hakoran yin cizo.

Afrika

Post navigation

Previous Post: Shirin Dare 2030 UTC Yau Alhamis 11.20.2025
Next Post: Ba Shakka Najeriya Zata Iya Shiga Gasar Harbi Ta Duniya

Karin Labarai Masu Alaka

Janar Rabe Abubakar Ya Mutu A Tsare A Hannun Masu Garkuwa Da Mutane Afrika
Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS Afrika
CNG Ta Farfado Da Jarin Masu Adaidaita Sahu A Kaduna Afrika
Shugaban Majalisar Tarayyar Turai Yace Rasha Tana Cin Ribar Yakin Gabas Ta Tsakiya Afrika
Ruwan Sama Yayi Ajalin Daruruwan Mutane A Afirka Ta Kudu Afrika
Afirka Ta Kudu Ta Bukaci Jakadan Israela Ya Fice Daga Kasar Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Wani Harin ‘Yan Bindiga Ya Kashe Mutane 35 A Jihar Borno Labarai
  • FIFA, Ta Raba Jaddawalin Rukuni Na Gasar Kofin Duniya 2026. Wasanni
  • Kasar Netherland Ta Mayarwa Masar Mutum Mutumin Tarihi Afrika
  • Shugaban Amurka Ya Sauke Antoni Janar Amurka
  • Yau Litinin Ake Cigaba Da Shari’ar Najib Zarak Labarai
  • Amurka Ta Kai ‘Yan Cirani Kamaru Afrika
  • Jiragen Ruwa Suna Biyayya Ga Dokar Hana Ketare Ruwa Amurka
  • ‘Yan Bindiga Sun Hallaka Mutane 30 A Jihar Neja Najeriya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.