Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Amurka Na Shirin Kauracewa Taron Kungiyar Kasashen G20
Published: November 21, 2025 at 4:36 AM | By: Yusuf Aliyu Harande

Fadar shugaban Amurka ta White House ta musanta kalamun da shugaba Cyril Ramaphosa na Afrika Ta Kudu (ATK) yayi jiya Alhamis inda yake cewa Amurka tana tunanin canja ra’ayinta game da kauracewa taron kolin kasashen kungiyar G20 a birnin Johannesburg.

A wajen wani taron manema labarai da manyan jami’an Kungiyar Tarayyar Turai jiya alhamis, shugaba Ramaphosa yace sun samu wata sanarwa daga Amurka game da canja ra’ayi ko kuma dai halartar taron a wani matsayi.

Wata jami’ar White House ta musanta wannan, tana mai cewa karamin jakadan Amurka dake Pretoria zai je wurin taron ne domin karbar ragamar jagorancin kungiyar na karba-karba wanda zai komo hannun Amurka, amma ba wai don halartar wani abu na taron ba.

Gwamnatin shugaba Trump ta ce Amurka ba zata halarci taron farko na kungiyar G20 da za a yi a Afirka ba, tana mai zargin cewa ATK mai masaukin baki, wadda turawa ‘yan tsiraru na kasar suka mulke ta har zuwa 1994, tana gallazawa da cin mutuncin turawan kasar.

Ita dai kungiyar ta G20, kungiya ce ta kasashe 19 da suka kunshi wadanda suka fi arziki da kuma wadanda tattalin arzikinsu ke tasowa sosai. A shekarar 2023, KTT da KTA, sun shiga a zaman membobi masu wakiltar kasashensu, kungiyar ta zamo mai membobi 21.

Wannan kungiya, ba kamar kungiyar G7 ta kasashe mafiya arziki zalla ba, tana mayarda hankulanta ne kan tattalin arzikin duniya da ayyukan raya kasa. Sai dai kungiyar ba ta da hedkwata, kuma ba ta cimma shawarwarin da dole membobi suyi aiki da su, abinda ya sa masu sukar lamiri suke ce kungiyar haushi kawai ta iya, ba ta da hakoran yin cizo.

Afrika

Post navigation

Previous Post: Shirin Dare 2030 UTC Yau Alhamis 11.20.2025
Next Post: Ba Shakka Najeriya Zata Iya Shiga Gasar Harbi Ta Duniya

Karin Labarai Masu Alaka

Kudin Man Fetur Ya Karu Da Kashi 10 Cikin 100 Afrika
An Kama Masu Fasa Kaurin Gawayi A Malawi Afrika
Malaman Addinin Musulunci Da Kirista Sunyi Bikin Cika Shekara 15 Na Iftar A Najeriya Afrika
Jama’ar Kasar Iran Sun Bayyana Goyon Baya Ga Ayatollah Mojtaba Khameni Afrika
Magoya Bayan Tijjaniyya Zasu Kauracewa Zabe Saboda Kama Sheikh Sani Khalifa Afrika
Sanarwar MDD Ya Nuna Aniyar Mayakan RSF Na Kisan Kare Dangi Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Kungiyar Gwamnonin Arewacin Najeriya Tayi Kakkausar Lafazi Game Da Harin Maiduguri
  • Tinubu, Akpabio da Ministoci 9 Zasu Tafi Ƙasar Birtaniya
  • Tinubu Ya Aika Manyan Hafsoshin Tsaro Borno
  • Lauyoyi Sun Gurfanar Da Wani A Kotu Bisa Fasa Korin Kiyashi A Kenya
  • Anfara Gangamin Kafa Dokoki Masu Tsanani Ga ‘Yan Luwadi A Senegal

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Alhassan Yayi Nasarar Kifar Da Wurkilili A Gasar Damben Gargajiya Wasanni
  • Kungiyar ECOWAS Ta Koka Game Da Yawan Juyin Mulki A Kasashen Afirka Afrika
  • Okoye Na Shirin Maye Gurbin Nwabali, AFCON 2025: Wasanni
  • Jirgin Dakon Iskar Gas Daga Rasha Ya Sake Hanya Afrika
  • Shirin: Lafiya Jari Ce 11.21.25 Kiwon Lafiya
  • Hukumar Zabe A Kasar Honduras Ta Sanar Da Nasry Asfura A Matsayin Wanda Ya Lashe Zaben Shugaban Ƙasa Afrika
  • Kenya Ta Cimma Yarjejeniya Da Kasar Rasha Afrika
  • Amurka Ta Kwace Jirgin Mai Mallakar Rasha Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.