Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19 Afrika
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027 Afrika
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki Afrika
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko Afrika

Yau Litinin Ake Cigaba Da Shari’ar Najib Zarak
Published: December 22, 2025 at 9:09 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Ranar litinin tsohon fira ministan kasar Malaysia, Najib Razak, zai san ko zai iya karasa sauran hukuncin daurin da aka yanke masa a gidansa, ko kuma a cikin kurkuku.

An yanke ma Razak hukuncin daurin shekaru 12 a gidan kurkuku a shekarar 2022, bisa laifin zarmiya da cin hanci a badakalar da aka fi sani da sunan abin Fallasa na 1MDB.

A shekarar da ta shige, wata hukumar yahudawa dake karkashin jagorancin tsohon Sarkin Malaysia, ta rage masa hukumcin zuwa shekaru 6.

Amma Razak ya ce Sarkin na Malaysia ya kuma bada umurnin cewa yana iya karasa wannan hukuncin a gidansa, watau daurin talala, kuma abinda ya sa ya shigar da kara ke nan a kotu yana neman a yi aiki da wannan umurnin da gwamnatin fira minista Anwar Ibrahim ta ce ba ta san da shi ba.

Jami’an gwamnati sunyi wata da watanni suna cewa ba su da wata masaniya game da wannan takardar umurni, duk da cewa a cikin wannan shekara, ofishin tsohon sarkin da ma wani lauya na tarayya sun gaskata cewa lallai an bayar da takardar umurnin rege hukumcin zuwa shekaru 6, kuma za a iya kyale ya karasa a gidansa.

Ranar litinin, babbar kotun birnin Kuala Lumpur zata yanke hukumci a kan wannan, kwanaki hudu kafin ta yanke hukunci a kan shari’a mafi girma da shi Najib yake fuskanta dangane da wannan abin fallasa na asusun 1Malaysia Development Berhad, wanda asusu ne na kudin gwamnati da ya taimaka wajen kirkirowa a shekarar 2009.

Masu fashin baki suka ce mutane ba zasu yi murna ba, musamman magoya bayan fira minista Anwar, idan kotun ta wanke shi a wancan zargin, Anwar dai ya ci zabe ne bisa alkawarin yaki da cin hanci da rashawa.

Labarai

Post navigation

Previous Post: Rasha Ta Nuna Kudurin Cimma Zaman Lafiya Da Ukraine
Next Post: Ministocin Kasar Asia Zasu Gudanar Da Taro A Kasar Malaysia

Karin Labarai Masu Alaka

Yakin Gabas Ta Tsakiya Ya Kawo Cikas Ga Cinikin Nama A Kenya Afrika
Bankin Duniya Ya Rage Hasashen Bunkasar Tattalin Arzikin Afirka Da Yankin Sahara Afrika
NUJ Gombe Ta Ƙarfafa Bin Ɗa’a A Aikin Jarida, Ta Kaddamar Da Kwamitin Ladabtarwa Afrika
Kasar Saudiya Zata Cika Azumi Talatin Kimiya
Afrika Ta Kudu Ta Dora Haraji Mai Yawa Kan Karafa Afrika
Shugaba Putin Ya Bukaci Kawo Karshen Yaki Da Iran Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Tinubu Ya Rantsar Da Shugabar Hukumar FCC Najeriya
  • Nuhu Ribadu Ya Mika Dalibai 100 da Aka Ceto Ga Gwamnatin Jihar Neja Labarai
  • Shugaban Kasar Uganda Yana Kokarin Mayar Da Mulkin Kasar Na Gado Labarai
  • Rundunar Sojin Najeriya Ta Kubutar Da Wasu Mutane 31 Da Aka Yi Garkuwa Dasu Afrika
  • Iran Tabada Tabbacin Cigaba Da Rufe Mashigar Hormuz Afrika
  • Shirin Safe 0500 UTC Yau Litinin 11.17.2025 Rediyo
  • Kudin Man Fetur Ya Karu Da Kashi 10 Cikin 100 Afrika
  • Guinea An Zabi Madugun Sojojin Da Suka yi Juyin Mulki Mamady A Shugaban Ƙasar, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.