Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • APC: Tinubu Da Shettima Za Su Sake Neman Wa’adi Na Biyu A 2027 Afrika
  • Sabuwar Sakatariyar Ƙungiyar Gwamnonin Arewa Za Ta Ƙarfafa Ayyukan Ci Gaban Yankin Afrika
  • TIC Dutse Ta Nemi Ƙarin Tallafin Gwamnatin Jigawa Don Faɗaɗa Ayyukanta Afrika
  • Gobara Ta Lalata Babban Zauren Majami’ar ECWA Gospel A Gombe Afrika
  • Gombe: ‘Yan Sanda Sun Tarwatsa Ƙungiyar Masu Fashi Da Damfara Ta Yanar Gizo Afrika

An Binne Gawar Tsohon Shugaban Sashen Hausa Na VOA, Leo Keyen
Published: July 4, 2026 at 4:33 PM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: July 4, 2026

An binne gawar tsohon shugaban Sashen Hausa na Gidan Rediyon Muryar Amurka (VOA), Leo Keyen, yayin da ‘yan’uwa, abokan aiki da abokan arziki suka yi masa bankwana tare da bayyana shi a matsayin ƙwararren ɗan jarida, shugaba nagari, kuma mai jajircewa wajen bunƙasa aikin jarida da raya matasa.

Marigayi Leo Keyen ya rasu ne a ranar 22 ga Yunin 2026, yana da shekaru 70 a duniya, bayan ya shafe kusan shekara goma sha ɗaya yana fama da cutar Parkinson’s Disease.

Da yake jawabi, ɗan’uwan marigayin, Injiniya Noel Keyen, ya ce rasuwar ta yi wa iyali da abokansa babban rashi, amma sun amince da hukuncin Allah.

Marigayi Leo Keyen ya yi aiki a cibiyoyin yaɗa labarai da dama, ciki har da NTA da JIB, sannan ya kasance Daraktan Yaɗa Labarai na Jam’iyyar PDP ta ƙasa a zamanin marigayi Solomon Lar. Haka kuma, ya taba zama Babban Daraktan Gidan Rediyo da Talabijin na Jihar Filato (PRTV) sau biyu.

Daga shekarar 2011 zuwa 2018, Leo Keyen ya jagoranci Sashen Hausa na VOA, inda ya faɗaɗa ayyukan rediyo, talabijin da kafafen yanar gizo, lamarin da ya ƙara yawan masu sauraro da masu kallo a Najeriya, Nijar, Kamaru, Chadi da sauran ƙasashe.

Wasu daga cikin shirye-shiryen da ya assasa sun haɗa da Dandalin VOA, Taskar VOA da kuma Tattaunawa, waɗanda suka mayar da hankali kan siyasa, shugabanci da harkokin tsaro.

Tsohon Shugaban Gidauniyar Horas da Ma’aikata ta ITF, Sir Joseph Ari, ya ce ƙwarewar Leo Keyen ta taimaka wajen samar da ingantattun labarai da shirye-shiryen da suka amfani al’umma.

Shi ma tsohon abokin aikinsa a VOA, Malam Sahabo Imam Aliyu, ya bayyana marigayin a matsayin shugaba mai adalci da nagarta, yayin da Hajiya Madina Dauda Nadabo ta ce Leo Keyen mutum ne da bai nuna bambanci tsakanin ma’aikatansa.

Baya ga aikin jarida, marigayin ya kasance mai ƙarfafa gwiwar matasa wajen shiga harkokin kasuwanci da dogaro da kai.

A nasa jawabin, Hon. Kefiano Kefas Ropshik ya yi kira ga al’umma da su ci gaba da kula da iyalan marigayin tare da tuna gudunmawar da ya bayar ga ci gaban aikin jarida.

Marigayi Leo Keyen ya rasu ya bar matarsa guda ɗaya, ‘ya’ya huɗu da jikoki uku. Allah Ya jikansa da rahama. Ameen.

Ga Rahoton Wakiliyar GTA Hausa Amurka Ke Magana Zainab Babaji Daga Jos

https://gtahausa.com/wp-content/uploads/2026/07/AUD-20260704-WA0020.mp3
Afrika, Labarai, Najeriya, Rumbun Hotuna

Post navigation

Previous Post: ‘Yan Jaridar Gidan Gwamnatin Bauchi Sun Kammala Taron Horo Kan Fasahar Sadarwar Zamani
Next Post: Rangadin Ayyukan Tinubu Ya Kai Tawaga Zuwa Kano Northern Bypass

Karin Labarai Masu Alaka

Netanyahu Ya Umarci Rundunar Sojoji Takara Fadada Ayyukanta A Lebanon Afrika
Yan Najeriya na ci gaba da maida martani akan sabuwar dokar zabe da majalisar Dattawan kasar ta Amince dashi Najeriya
Gwamnatin Gombe Ta Kulla Yarjejeniyar Da New Zealand Kimiya
Kungiyar Gwamnonin Arewacin Najeriya Tayi Kakkausar Lafazi Game Da Harin Maiduguri Afrika
Gwamna Inuwa Yahaya Ya Bukaci Al’ummar Gombe Su Haɗa Kai Wajen Yaƙi Da Ta’addanci Afrika
Yau Litinin Za’a Mika Daliban Ga Iyayen Su Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • APC: Tinubu Da Shettima Za Su Sake Neman Wa’adi Na Biyu A 2027
  • Sabuwar Sakatariyar Ƙungiyar Gwamnonin Arewa Za Ta Ƙarfafa Ayyukan Ci Gaban Yankin
  • TIC Dutse Ta Nemi Ƙarin Tallafin Gwamnatin Jigawa Don Faɗaɗa Ayyukanta
  • Gobara Ta Lalata Babban Zauren Majami’ar ECWA Gospel A Gombe
  • Gombe: ‘Yan Sanda Sun Tarwatsa Ƙungiyar Masu Fashi Da Damfara Ta Yanar Gizo

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Mataimakin Shugaban Kasa Ya Sauka A Jihar Kwara Labarai
  • Sojojin Kasar Uganda Sun Bazama Neman Bobi Wine Sakamakon Rikicin Bayan Zabe Siyasa
  • Gwamna Ahmad Aliyu Na Jihar Sokoto Ya Gabatar Da Kasafin Fiye Da Naira Biliyan 700 Labarai
  • Yusuf Gawuna Ya Koma Jam’iyar ADC Afrika
  • Farashin Mai Yana Cigaba Da Karuwa Afrika
  • Amurka Ta Kai ‘Yan Cirani Kamaru Afrika
  • Hukumar ‘Yan Sanda Ta Bukaci Jama’ar Jos Ta Arewa Su Rika Bin Doka Afrika
  • Sakataren Tsaron Amurka Ya Kori Shugaban Sojin Kasar Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.