Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • APC: Tinubu Da Shettima Za Su Sake Neman Wa’adi Na Biyu A 2027 Afrika
  • Sabuwar Sakatariyar Ƙungiyar Gwamnonin Arewa Za Ta Ƙarfafa Ayyukan Ci Gaban Yankin Afrika
  • TIC Dutse Ta Nemi Ƙarin Tallafin Gwamnatin Jigawa Don Faɗaɗa Ayyukanta Afrika
  • Gobara Ta Lalata Babban Zauren Majami’ar ECWA Gospel A Gombe Afrika
  • Gombe: ‘Yan Sanda Sun Tarwatsa Ƙungiyar Masu Fashi Da Damfara Ta Yanar Gizo Afrika

Rangadin Ayyukan Tinubu Ya Kai Tawaga Zuwa Kano Northern Bypass
Published: July 5, 2026 at 4:53 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Tawagar masu yaɗa labarai da ke halartar shirin Arewa Media Summit ta kai ziyara zuwa aikin gina Kano Northern Bypass, a ci gaba da rangadin manyan ayyukan gwamnatin tarayya da ake aiwatarwa a Jihar Kano ƙarƙashin jagorancin Shugaba Bola Ahmed Tinubu.

Rangadin ya gudana ne bisa jagorancin Ofishin Babban Mai Taimakawa Shugaban Ƙasa kan Harkokin Yaɗa Labarai da Wayar da Kan Jama’a, Malam Abdulaziz Abdulaziz, domin bai wa mahalarta taron damar ganin ci gaban ayyukan raya ƙasa da gwamnatin tarayya ke gudanarwa a Arewacin Najeriya.

Aikin Kano Northern Bypass, mai tsawon kusan kilomita 38, ya taso daga hanyar Kano–Hadejia zuwa hanyar Kano–Katsina. Ana sa ran kammala aikin zai rage cunkoson manyan motoci da ke bi ta cikin birnin Kano tare da sauƙaƙa zirga-zirgar kayayyaki da fasinjoji.

Masana sun bayyana cewa aikin zai rage asarar lokaci da kuɗaɗen sufuri, ya bunƙasa harkokin kasuwanci da masana’antu, tare da ƙara jawo masu zuba jari zuwa yankunan Zaura, Dawanau, Tarda da sauran al’ummomin da ke kewaye da hanyar.

Haka kuma, ana hasashen aikin zai samar da sabbin guraben ayyukan yi ga matasa da kuma ƙarfafa tattalin arzikin jihar da ma yankin Arewa baki ɗaya.

Masu shirya Arewa Media Summit sun ce rangadin na ba ‘yan jarida da masu tasiri a kafafen sada zumunta damar ganin ayyukan da ido, domin su samar wa al’umma sahihan rahotanni masu dogaro da hujjoji kan ci gaban da ake samu a ƙarƙashin Ajandar Renewed Hope ta Shugaba Bola Ahmed Tinubu.

Ana sa ran taron Arewa Media Summit zai gudana ranar 6 ga Yulin 2026 a Coronation Hall da ke Gidan Gwamnatin jihar Kano, inda zai haɗa manyan ‘yan jarida, masana, masu tasiri da sauran masu ruwa da tsaki domin tattauna rawar kafafen yaɗa labarai wajen bunƙasa ci gaban Arewa da Najeriya baki ɗaya.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Nishadi, Sauran Duniya, Siyasa

Post navigation

Previous Post: An Binne Gawar Tsohon Shugaban Sashen Hausa Na VOA, Leo Keyen
Next Post: Gombe Da UNFPA Sun Ƙarfafa Haɗin Gwiwa Don Yaƙi Da Cutar Fistula Da Tamowa

Karin Labarai Masu Alaka

Ana Cigaba Da Shirye-Shiryen Fara Gasar Kwallon Sarakuna A Gombe Afrika
Tattalin Arzikin Najeriya Ya Farfardo Bisa Samun Wasu Sauye Sauye Labarai
Fiye Da Mutane 10 Sun Mutu A Hatsarin Hanyar Kano Labarai
‘Yan Jaridar Gidan Gwamnatin Bauchi Sun Kammala Taron Horo Kan Fasahar Sadarwar Zamani Afrika
Iran Ta Rufe Sararin Samaniyar Ta Labarai
Lakurawa Sun Kashe A Ƙalla A Mutane 34 A Jihar Kebbi Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • APC: Tinubu Da Shettima Za Su Sake Neman Wa’adi Na Biyu A 2027
  • Sabuwar Sakatariyar Ƙungiyar Gwamnonin Arewa Za Ta Ƙarfafa Ayyukan Ci Gaban Yankin
  • TIC Dutse Ta Nemi Ƙarin Tallafin Gwamnatin Jigawa Don Faɗaɗa Ayyukanta
  • Gobara Ta Lalata Babban Zauren Majami’ar ECWA Gospel A Gombe
  • Gombe: ‘Yan Sanda Sun Tarwatsa Ƙungiyar Masu Fashi Da Damfara Ta Yanar Gizo

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Abun Da Kuke Buƙatar Sani Game Da Gasar Cin Kofin Ƙasashen Afirka 2025 Wasanni
  • Tattalin Arzikin Kasar Congo Ya Bunkasa Labarai
  • An Fara Dawo Da Alhazain Najeriya Gida Afrika
  • ‘Yan Tawayen Houthi Sunkai Hari Isra’ila Afrika
  • An Katse Intanet Da Wayar Tarho A Kasar Uganda Siyasa
  • Iran: Za A Gudanar Da Jana’izar Khamenei Bayan Kwanaki Goma Na Muharram Afrika
  • Ahmed Gara Ya Kaddamar da Kofin Sarkin Gombe, Ya Jaddada Bunƙasa Matasa Afrika
  • Shugaban Majalisar Tarayyar Turai Yace Rasha Tana Cin Ribar Yakin Gabas Ta Tsakiya Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.