Tawagar masu yaɗa labarai da ke halartar shirin Arewa Media Summit ta kai ziyara zuwa aikin gina Kano Northern Bypass, a ci gaba da rangadin manyan ayyukan gwamnatin tarayya da ake aiwatarwa a Jihar Kano ƙarƙashin jagorancin Shugaba Bola Ahmed Tinubu.
Rangadin ya gudana ne bisa jagorancin Ofishin Babban Mai Taimakawa Shugaban Ƙasa kan Harkokin Yaɗa Labarai da Wayar da Kan Jama’a, Malam Abdulaziz Abdulaziz, domin bai wa mahalarta taron damar ganin ci gaban ayyukan raya ƙasa da gwamnatin tarayya ke gudanarwa a Arewacin Najeriya.

Aikin Kano Northern Bypass, mai tsawon kusan kilomita 38, ya taso daga hanyar Kano–Hadejia zuwa hanyar Kano–Katsina. Ana sa ran kammala aikin zai rage cunkoson manyan motoci da ke bi ta cikin birnin Kano tare da sauƙaƙa zirga-zirgar kayayyaki da fasinjoji.

Masana sun bayyana cewa aikin zai rage asarar lokaci da kuɗaɗen sufuri, ya bunƙasa harkokin kasuwanci da masana’antu, tare da ƙara jawo masu zuba jari zuwa yankunan Zaura, Dawanau, Tarda da sauran al’ummomin da ke kewaye da hanyar.
Haka kuma, ana hasashen aikin zai samar da sabbin guraben ayyukan yi ga matasa da kuma ƙarfafa tattalin arzikin jihar da ma yankin Arewa baki ɗaya.
Masu shirya Arewa Media Summit sun ce rangadin na ba ‘yan jarida da masu tasiri a kafafen sada zumunta damar ganin ayyukan da ido, domin su samar wa al’umma sahihan rahotanni masu dogaro da hujjoji kan ci gaban da ake samu a ƙarƙashin Ajandar Renewed Hope ta Shugaba Bola Ahmed Tinubu.
Ana sa ran taron Arewa Media Summit zai gudana ranar 6 ga Yulin 2026 a Coronation Hall da ke Gidan Gwamnatin jihar Kano, inda zai haɗa manyan ‘yan jarida, masana, masu tasiri da sauran masu ruwa da tsaki domin tattauna rawar kafafen yaɗa labarai wajen bunƙasa ci gaban Arewa da Najeriya baki ɗaya.


