Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19 Afrika
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027 Afrika
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki Afrika
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko Afrika

An Damke Matasa Masu Gurza Kudaden Ketare Na Jabu
Published: November 21, 2025 at 11:27 PM | By: Yusuf Aliyu Harande

Jami’an tsaro a Jamhuriyar Nijar sun dakile wani yunkurin baza kudaden Jabu a harakokin hada hadar kudaden kasar.
Dubban takardun Euro da a ka kyasta cewa darajarsu ta haura milion 600 na CFA ne a ka cafke a hannun wasu matasa a birnin Yamai, lamarin da ya sa al’umma ta jinjinawa jami’an tsaro tare da jan hankulan hukumomi su karfafa matakan tsaro.
Bayanan sirrin da rundunar tsaron Garde Nationale ta bibiya ne suka bai wa dakarunta damar gano wani gida da ke anguwar Nord Lazaret ta birnin Yamai inda ake buga takardun kudade na Jabu.
A yayin samamen da suka kai jami’an tsaro sun kama wasu mutane biyu dukkansu matasan masu kimanin shekaru 30, an same su dauke da dubban takardun kudaden Euro dari biyu-biyu, hade da wasu sinadaran da aka ayyana a matsayin na wankin takardar kudi.
Da ta ke  bayyana ra’ayinta kan wannan al’amari Mme Adji Gana Fatouma Souleymane na cewa.
“An kyasta cewa darajar wadanan takardun kudaden Euro na Jabu sun haura milion 600 na CFA wadanda idan aka yi nasarar shigar da su, babbar barzana ce ga tattalin arziki” inji sakataren watsa labaran kungiyar FRSA Salissou Ibrahim.
Buga kudin Jabu na daga jerin miyagun aiyukan da a ka gano cewa suna kokarin samun gindin zama a Nijar, abin da wani mazaunin Yamai Laouali Boubacar yace ya kamata hukumomi su taka musu burki tun da wuri.
Mutanen da rundunar tsaron ta Garde Nationale ta kama ko ba ya ga takardun kudaden Jabu an same su da kakin Soja da tufafin wasannin motsa jiki masu dauke da tambarin ‘yan Sanda.
Afrika

Post navigation

Previous Post: Shirin Manuniya Kashi Na Daya, Yau Juma’a 11.21.25
Next Post: Manya-Manyan Wasannin Wannan Makon

Karin Labarai Masu Alaka

Hukumomi A Kasar Syri Lanka Suna Kokarin Fidda Jirgin Yakin Iran Daga Kasar Afrika
Gwamnatin Najeriya Ta Tallafa Wa ’Yan Sanda Da Motoci Afrika
Ministan Sufurin Najeriya Ya Ajiye Mukaminsa Domin Takarar Gwamna Afrika
Darajar Kudin Afirka Ta Kudu Ya Tashi Afrika
‘Yan Sandan Najeriya Sunyi Nasarar Hallaka ‘Yan Ta’adda A Katsina Afrika
Jami’an Shiga Da Fice A Afirka Ta Kudu Sun Tafka Badakalar Kudade Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Hukumar NAHCON Ta Kamallah Shirye Shiryen Hajjin 2026 A Kasar Saudiya Labarai
  • Trump: Zamu Kawo Zaman Lafiya A Fadin Duniya Amurka
  • Mayakan RSF Sun Zafafa Kai Hare Hare Da Jirgi Maras Matuki A Sudan Labarai
  • Tawagar IMF Tana Kasar Kenya Domin Tattauna Bada Lamuni Labarai
  • Bayan Shekaru Biyar, Rundunar ‘Yan Sandan Gombe Ta Gano Motar da Aka Sace A Fatakwal Afrika
  • Kocin Ranchers Bees Ya Yi Murabus Wasanni
  • Tsohon Gwamnan Kano, Malam Ibrahim Shekarau Ya Koma Jam’iyyar APC Afrika
  • Hukumar ‘Yan Sanda Ta Bukaci Jama’ar Jos Ta Arewa Su Rika Bin Doka Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.