Ministan Sufuri, Sanata Saidu Ahmed Alkali, ya mika takardar murabus dinsa a hukumance ga Fadar Shugaban Kasa.
Sanarwar Umar Alkali Jibril Mataimaki na Musamman kan Kafofin Yada Labarai ga Ministan ta bayyana cewa, wannan mataki ya biyo bayan umarnin Shugaban Kasa ne da ya bukaci dukkan masu rike da mukaman siyasa masu sha’awar tsayawa takara a zabe mai zuwa da su sauka daga mukamansu.
Ministan ya yi murabus ne domin ya tsaya takarar gwamna a jihar Gombe a zabuka masu zuwa. A cikin takardar tasa, ya bayyana godiyarsa ga Shugaban Kasa bisa damar da aka ba shi na yin hidima, inda ya bayyana gagarumar nasarar da aka samu a fannin sufuri a lokacin jagorancinsa.
Shugaban Kasa ya amince da murabus din nasa, sannan ya gode wa Ministan bisa jajircewarsa wajen yi wa kasa hidima.


