Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sauya Sunan Lafarge Africa Zuwa HBM Nigeria Plc Zai Samar Da Cigaba – Sarkin Fulanin Gombe Afrika
  • An Karrama Darakta Janar Na DSS Bisa Ƙoƙarinsa Na Inganta Alaƙar Hukumomin Tsaro Da Kafafen Yaɗa Labarai Afrika
  • Gwamnatin Tarayyar Najeriya Zata Raba Taki Ga Manoma Afrika
  • Makokin Ashura: An Gudanar Da Taron Tunawa Da Aliyul Asghar A Gombe Afrika
  • Rashin Hanya da Asibiti Ya Jawo Asarar Rayuka A Jihar Gombe – Sarkin Gargajiya Afrika

Bayan Shekaru Biyar, Rundunar ‘Yan Sandan Gombe Ta Gano Motar da Aka Sace A Fatakwal
Published: June 20, 2026 at 9:49 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

A cikin wata sanarwa da Jami’in Hulɗa da Jama’a na Rundunar, DSP Buhari Abdullahi, ya fitar, ya bayyana cewa jami’an Sashen Binciken Sirri (SID) na rundunar, tare da haɗin gwiwar jami’an Hukumar Kiyaye Haɗurra ta Ƙasa (FRSC), sun gano motar ne yayin wani aikin tantance bayanan motoci a Ofishin Ba da Lasisin Motoci na Hukumar Haraji ta Jihar Gombe a ranar 8 ga Yunin 2026.

Sanarwar ta ce yayin binciken bayanan motar mai lambar rajista FH823PHC, an gano alamun da suka nuna cewa motar na da alaƙa da rahoton sata.

Binciken farko ya tabbatar da cewa motar mallakin Misis Cecilia A. Duru ce, mazauniyar Akwaka Lane da ke Rumuodumaya a Fatakwal, kuma an sace ta ne a ranar 17 ga Satumban 2021.

Binciken da rundunar ta gudanar ya nuna cewa an kai motar zuwa Jamhuriyar Nijar a shekarar 2023. Daga bisani kuma an dawo da ita Najeriya ta Karamar Hukumar Illela da ke Jihar Sokoto a ranar 17 ga Oktoban 2025.

Bayan haka, an sayar da motar a Jihar Kaduna kafin daga ƙarshe a kawo ta Gombe domin sake yi mata rajista.

Rundunar ta ce bincike na ci gaba da nufin gano tare da cafke duk waɗanda ake zargi da hannu a satar motar da kuma safararta ba bisa ƙa’ida ba.

Haka kuma, rundunar ta tabbatar wa al’umma da cewa za ta ci gaba da ɗaukar matakan kare rayuka da dukiyoyi, tare da jan hankalin masu sayen motoci da su tabbatar da sahihancin takardun mallaka da bayanan mota daga hukumomin da suka dace kafin su kammala ciniki.

Sanarwar ta ƙara da cewa za a sanar da jama’a duk wani sabon ci gaba da aka samu yayin da bincike ke gudana.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Sauran Duniya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Makokin Ashura: An Gudanar Da Taron Tunawa Da Aliyul Asghar A Gombe
Next Post: Gwamnatin Tarayyar Najeriya Zata Raba Taki Ga Manoma

Karin Labarai Masu Alaka

Afirka Ta Kudu Ta Kubutar Da ‘Yan Kasar Da Suke Taya Sojojin Rasha Yaki Afrika
Tinubu Ya Buƙaci Gwamnoni Su Mutunta Hukuncin Kotun Ƙoli Kan ’Yancin Kuɗin ƙananan Hukumomi Labarai
Tinubu Ya Maye Gurbin Badaru Da Tsohon Soja Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Gobara Mafi Muni Cikin Shekaru 60 A Hong Kong Ta Hallaka Rayuka Sauran Duniya
Gwamna Zulum: Ya Bukaci Sojoji Su Cigaba Da Yakar Boko Haram Da ISWAP Labarai
Yajin Aikin Ma’aikatan Lafiya Na Shafar Harkokin Jinya A Asibitoci Kiwon Lafiya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sauya Sunan Lafarge Africa Zuwa HBM Nigeria Plc Zai Samar Da Cigaba – Sarkin Fulanin Gombe
  • An Karrama Darakta Janar Na DSS Bisa Ƙoƙarinsa Na Inganta Alaƙar Hukumomin Tsaro Da Kafafen Yaɗa Labarai
  • Gwamnatin Tarayyar Najeriya Zata Raba Taki Ga Manoma
  • Bayan Shekaru Biyar, Rundunar ‘Yan Sandan Gombe Ta Gano Motar da Aka Sace A Fatakwal
  • Makokin Ashura: An Gudanar Da Taron Tunawa Da Aliyul Asghar A Gombe

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Amurka Tayi Barazanar Rage Tallafinta Wa Sudan Ta Kudu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Gombe Zata Inganta Samar Da Wuta Wajen Amfani Da Hasken Rana Kimiya
  • Iran Tabada Tabbacin Cigaba Da Rufe Mashigar Hormuz Afrika
  • Amurka Zata Saidawa Saudiyya Da Jirgin Yaki Samfurin F35 Labarai
  • Muna Kira Ga Kasashen Duniya Su Sa Baki Don A Saki Mohamed Bazoum Afrika
  • Kasar China Tana Cigaba Da Nuna Fin Karfi Ga Kasar Taiwan Labarai
  • Kamfanin Hakar Ma’adanai Na Kasar Kanada Ya Cigaban Da Aikinsa Labarai
  • Ana Cigaba Da Tattaunawa Tsakanin Trump Da Zelensky Domin Tsagaita Wuta A Ukraine Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.