Mahalarta Taron Tsaro na Ƙasa da Ƙungiyar ‘Yan Jarida ta Najeriya (NUJ) tare da haɗin gwiwar Hukumar Tsaro ta Farin Kaya (DSS) suka shirya a Abuja, sun yi kira da a ƙara ƙarfafa haɗin gwiwa tsakanin kafafen yaɗa labarai da hukumomin tsaro domin fuskantar ƙalubalen tsaron da ƙasar ke fama da su tare da inganta ci gaban ƙasa.

An bayyana hakan ne a cikin sanarwar bayan taron na kwanaki biyu da aka gudanar daga ranar 18 zuwa 19 ga watan Yunin 2026, mai taken “Kafafen Yaɗa Labarai da Hukumomin Tsaro a Matsayin Abokan Hulɗa wajen Gina Ƙasa.”

Taron ya haɗa manyan shugabannin kafafen yaɗa labarai, ‘yan jarida, shugabannin hukumomin tsaro da leƙen asiri, jami’an gwamnati, masana, ƙungiyoyin fararen hula, ƙungiyoyin mata da kuma abokan hulɗar ci gaba domin tattauna batutuwan tsaro, sadarwa mai tasiri, gina zaman lafiya da inganta dimokuraɗiyya.

Da yake jawabi a wajen buɗe taron, Shugaban Ƙungiyar ‘Yan Jarida ta Najeriya (NUJ), Comrade Alhassan Yahaya Abdullahi, ya bayyana taron a matsayin wani muhimmin mataki na tunkarar matsalolin tsaro da suka haɗa da ta’addanci, fashi da makami, garkuwa da mutane, laifukan yanar gizo, yaɗa bayanan ƙarya da rikice-rikicen al’umma.

Ya jaddada cewa tsaron ƙasa nauyi ne da ya rataya a wuyan kowa da kowa, yana mai ƙara da cewa aikin jarida mai bin ƙa’ida da gaskiya na taka muhimmiyar rawa wajen tabbatar da haɗin kan ƙasa, riƙon amana da zaman lafiya.
A nasa jawabin, Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kan Jama’a a Najeriya Alhaji Mohammed Idris, ya bayyana cewa kafafen yaɗa labarai da hukumomin tsaro suna da muhimmiyar rawa mai cike da alaƙa wajen gina ƙasa. Ya ce yayin da hukumomin tsaro ke da alhakin kare rayuka da dukiyoyi, kafafen yaɗa labarai kuwa suna zama idon al’umma da kuma gada tsakanin gwamnati da jama’a.

Taron ya kuma saurari gabatarwar masana daban-daban. Farfesa Okey Ikechukwu ya bayyana kafafen yaɗa labarai a matsayin wani muhimmin ginshiƙi da ke taimakawa nasarar ayyukan tsaro da ci gaban ƙasa. Haka kuma, Shugaban Cibiyar International Press Institute (IPI) ta Najeriya, Musikilu Mojeed, ya ce ‘yancin aikin jarida da tsaron ƙasa ginshiƙai ne guda biyu da ke ƙarfafa dimokuraɗiyya, kuma ya kamata a daidaita su cikin bin doka da ƙa’idojin sana’a.
A nata bangaren, Shugabar Ƙungiyar Mata ‘Yan Jarida ta Najeriya (NAWOJ), Aisha Ibrahim, ta yi kira da a bai wa mata dama sosai a harkokin gina zaman lafiya, hana rikice-rikice da kuma tafiyar da al’amuran tsaro.

Ɗaya daga cikin manyan abubuwan da suka ja hankali a taron shi ne karrama Darakta Janar na DSS, Mista Adeola Oluwatosin Ajayi, bisa gudummawar da yake bayarwa wajen ƙarfafa dangantaka tsakanin kafafen yaɗa labarai da hukumomin tsaro da kuma inganta tattaunawa da fahimtar juna domin amfanin ƙasa.
Mahalarta taron sun lura cewa Najeriya na ci gaba da fuskantar matsalolin tsaro masu sarkakiya, don haka suka buƙaci a rungumi tsarin da zai haɗa gwamnati, hukumomin tsaro, kafafen yaɗa labarai da al’umma baki ɗaya wajen magance matsalolin.
Daga cikin shawarwarin da taron ya bayar akwai samar da dandalin tattaunawa na dindindin tsakanin ‘yan jarida da hukumomin tsaro, inganta tsarin sadarwa domin yaƙi da yaɗa bayanan ƙarya, ƙarfafa tantance gaskiyar labarai, horas da jami’an tsaro da ‘yan jarida akai-akai, saka hannun jari a ilimi da samar da ayyukan yi ga matasa, da kuma ƙara bai wa mata damar taka rawa a harkokin tsaro da zaman lafiya.

Har ila yau, taron ya yi kira ga gwamnatocin jihohi da su ƙara tallafa wa kafafen yaɗa labarai na gwamnati domin inganta aikinsu, tare da roƙon Gwamnatin Tarayya da ta ƙara kuɗaɗen da ake warewa hukumomin tsaro domin bunƙasa amfani da fasahohin zamani, tattara bayanan sirri da inganta kayan aiki.

A ƙarshe, mahalarta taron sun jaddada cewa dorewar zaman lafiya, tsaro da ci gaban Najeriya na dogara ne da haɗin kai, amincewa da juna, gaskiya, riƙon amana da haɗin gwiwar dukkan masu ruwa da tsaki.


