Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

Ministan Yaɗa Labarai: Ceto Daliban Neja An Samu Natsuwa A Kasa
Published: December 11, 2025 at 7:56 AM | By: Bala Hassan | Updated: December 18, 2025

Ceto ɗaliban Neja ya dawo da natsuwa ga ƙasa, inji Ministan Yaɗa Labarai.

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris ya ce ceto ɗaliban da aka sace daga Makarantar Firamare da Sakandare ta St. Mary da ke Papyri, Jihar Neja, ya dawo da natsuwa da kwanciyar hankali ga iyalan su da ƙasa baki ɗaya.

Ministan ya bayyana hakan ne a ranar Laraba lokacin da ya jagoranci tawagar Gwamnatin Tarayya zuwa Fadar Gwamnatin Jihar Neja domin yin godiya da kuma bayyana jin daɗin dawowar yaran lafiya.

 

 

 

 

 

 

Tawagar ta samu tarbar Gwamnan Jihar Neja, Umaru Mohammed Bago.

Idris ya jaddada cewa haɗin kai tsakanin jami’an tsaro, Gwamnatin Jihar Neja da al’ummar yankin ne ya taimaka wajen nasarar aikin ceton.

Ya ce: “Ceton waɗannan yara ya dawo da natsuwa ga iyalan su da kuma ga ƙasa baki ɗaya. Mun yaba da jajircewar jami’an tsaro, saurin ɗaukar matakin Gwamnatin Jihar Neja, da kuma haɗin kan al’umma wanda ya ba da damar samun wannan sakamakon.”

Ministan ya kuma jaddada cewa gwamnatin Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ta ɗauki tsaron makarantu da kare ɗalibai da matuƙar muhimmanci.

Ya ƙara da cewa, “Dole ’ya’yan mu su samu damar yin karatu cikin tsaro. Gwamnatin Tarayya tana da cikakkiyar niyyar ci gaba da aiki tare da jihohi domin ƙarfafa tsaron makarantu, tare da tabbatar da cewa irin wannan ɓarna ga zaman lafiyar mu bai da wurin zama a ƙasar mu.”

A jawabin sa, Gwamna Bago ya gode wa Ministan bisa ziyarar, tare da yaba wa jami’an tsaro da al’ummomin yankin waɗanda suka taka rawa wajen ganin an sako ɗaliban.

Ya kuma jaddada cewa jihar za ta ci gaba da aiki tare da Gwamnatin Tarayya domin ƙarfafa tsaro da zaman lafiya.

Labarai

Post navigation

Previous Post: Amurka Ta Nuna Damuwa Kan Matsalar ‘Yan Gudun Hijira A Najeriya
Next Post: Gwamnatin Tarayya Tana Neman Kudi Domin Aiwatar Da Kasafin Kudin 2026

Karin Labarai Masu Alaka

Amurka Da Jamhuriyar Dimokraɗiyya Kwango Sun Fara Wata Tattaunawa Afrika
Gwamna Inuwa Yahaya Ya Amince Da Gyaran Fadar Sarkin Gombe Afrika
Gombe Ta Yi Fice A Duniya: Maryam Dan’azumi Ta Lashe Gasar Alƙur’ani Na Ƙasa Da Ƙasa Afrika
Maulidi: Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Ranar Hutu Afrika
Karancin Iskar Gas Kalubale Ne Ga Wutar Lantarki Labarai
Zelensky Na Ukraine Zai Gana Da Takwaransa Na Faransa A Yau Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Hukumar Kare Hakkin ‘Yan Jarida Tace Isra’ila Ce Ta Kashe ‘Yan Jarida Kashi Biyu Bisa Uku Labarai
  • An Garkame Wani Babban Soja A Kasar Australiya Afrika
  • An Saka Dokar Hana Fita A Jos Ta Arewa Afrika
  • Bisa Alamu Hadinkan Kasashen Yankin Sahel Zai Haifar Da Nagarta Afrika
  • Jihar Gombe Ta Karbi Bakuncin Taron Tsaro Tsakanin DIG Da Masu Ruwa Da Tsaki Afrika
  • Kungiyar HPV A Jihar Gombe Ta Jagoranci Yaki Da Karuwar Cutar Daji Afrika
  • Gwamnatin Kebbi Ta Samu Tankokin Yaki Tsaro
  • Tinubu: Munsayi Jiragen Yaki Daga Wajen Amurka Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.