Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe Afrika
  • Hukumomin Bada Agaji Sun Fadakar Da Al’ummar Jihar Gombe Afrika
  • Ana Cigaba Da Shirye-Shiryen Fara Gasar Kwallon Sarakuna A Gombe Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Zata Samar Da Sabbin Dakunan Karatun Dalibai Afrika
  • Gwamnatin Tarayya Ta Cire Sharadin Rubuta UTME Ga Masu Neman Shiga Kwalejojin Ilimi Afrika

Kungiyar HPV A Jihar Gombe Ta Jagoranci Yaki Da Karuwar Cutar Daji
Published: April 5, 2026 at 10:15 AM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: April 6, 2026

Kungiyar HPV ta jihar Gombe ta shirya wani gangamin wayar da kan al’umma, inda ta hada ‘yan jarida, ma’aikatan lafiya, masana ilimi, shugabannin al’umma da sauran masu ruwa da tsaki domin tunkarar barazanar karuwar cutar daji a jihar.

Da yake jawabi a wajen taron, Farfesa Muhammad Manga ya bukaci mahalarta su kirkiro dabaru masu amfani domin hana yaduwar cutar daji, musamman cutar sankarar mahaifa, da kuma yadda za a magance sauran nau’o’in cutar a cikin al’umma.

Ya bayyana cewa an hada bangarori daban-daban cikin shirin ne da gangan, musamman mambobin Kungiyar ‘Yan Jarida ta Najeriya, domin inganta tattaunawa da gano hanyoyin magance matsalolin cutar daji.

Farfesa Manga ya yaba wa mahalarta taron bisa jajircewarsu, yana mai jaddada cewa ana iya warkar da cutar daji idan aka gano ta da wuri. Ya kuma bukaci jama’a da su gaggauta neman kulawar likita idan sun lura da wasu sauye-sauye ko alamomi da ba su saba ba, tare da karfafa musu gwiwa su yada wannan sakon wayar da kai a cikin al’ummominsu.

Sauran masu jawabi, ciki har da shugabar taron, Dakta Halima Usman Farouk, Farfesa Danladi Adamu Bojude da Ferfesa Aliyu Lawal na Asibitin Koyarwa na Tarayya da ke Gombe, da kuma shugabannin al’umma Musa Mustafa da Danimoh Mustafa, sun jaddada bukatar kara hadin gwiwa tsakanin ‘yan jarida, ma’aikatan lafiya da sauran masu ruwa da tsaki domin yakar cutar daji yadda ya kamata.

Sun bayyana wasu daga cikin nau’o’in cutar daji da suka fi yawaita a jihar da suka hada da na mama, huhu, mafitsara ta maza, mahaifa, hanta, ciki, pankiriyas, koda, mafitsara, fata, kwakwalwa, ovaries, mahaifa ta mata da kuma esophagus.

Masu jawabin sun bukaci jama’a da su rika anfani da ayyukan kiwon lafiya da ake da su ta hanyar yin gwaje-gwaje akai-akai. Wadanda aka gano suna dauke da cutar an shawarce su da su nemi magani da wuri, yayin da sauran kuma aka karfafa musu gwiwa su yi allurar rigakafi inda ya dace.

Kungiyar ta sake jaddada kudirinta na kara fadada shirye-shiryen wayar da kai da kuma inganta samun damar ayyukan rigakafi domin rage mace-macen da ke da alaka da cutar daji a Jihar Gombe.

Daga jihar Gombe ga Rahoton Wakilin GTA Hausa Amurka Ke Magana Aliyu Bala Gerengi

https://gtahausa.com/wp-content/uploads/2026/04/HPV-GOMBE.mp3
Afrika, Kiwon Lafiya, Labarai, Najeriya, Rumbun Hotuna

Post navigation

Previous Post: Majalisar Dokokin Kamaru Ta Amince Da Wasu Sauye Sauye
Next Post: Rundunar Sojin Najeriya Ta Kubutar Da Wasu Mutane 31 Da Aka Yi Garkuwa Dasu

Karin Labarai Masu Alaka

Iran Ta Harbo Jiragen Yakin Amurka Biyu Amurka
Zelensky Na Ukraine Zai Gana Da Takwaransa Na Faransa A Yau Labarai
An Garkame Wani Babban Soja A Kasar Australiya Afrika
Gwamna Abba Kabir Ya Zabi Garo A Matsayin Mataimaki Afrika
Karo Na Biyu Cikin Kwanaki 29 An Samu Gobara A Kasuwar Katako Labarai
Libya Ta Kulla Yarjejeniya Da Kasashen Faransa Da Amurka Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe
  • Hukumomin Bada Agaji Sun Fadakar Da Al’ummar Jihar Gombe
  • Ana Cigaba Da Shirye-Shiryen Fara Gasar Kwallon Sarakuna A Gombe
  • Gwamnatin Najeriya Zata Samar Da Sabbin Dakunan Karatun Dalibai
  • Gwamnatin Tarayya Ta Cire Sharadin Rubuta UTME Ga Masu Neman Shiga Kwalejojin Ilimi

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Ga Dukkan Alamu Yaki Tsakanin Rasha Da Ukraine Bai Kare Ba Sauran Duniya
  • Hukumar Tsaron Teku A Libya Tafara Janye Jirgi Mai Dauke Da Iskar Gas Labarai
  • Babban Hafsan Tsaron Najeriya Ya Gargadi Jama’ar Arewa Maso Gabas Afrika
  • Shirin: Lafiya Jari Ce 11.21.25 Kiwon Lafiya
  • An Gudanar Da Idin Karamar Sallah A Birnin Niamey Labarai
  • Gabannin Harin Amurka Da Isra’ila Iran Farisa Ta Shirya Nata Afrika
  • Nasarawa Ce Zakara A Wasan Kwallon Kafa Ta Kurame 2025 Wasanni
  • Mizanin Tattalin Arzikin Najeriya Na 2024 Ya Karu Da Kashi 3.84% Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.