Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Tsohuwar Jarumar Kannywood Wasila Ismail Ta Rasu Afrika
  • Za’a Fassara Hudubar Arfa Da Harshen Hausa Afrika
  • An Kamallah Jigilar Alhazain Najeriya Domin Hajjin 2026 Afrika
  • Bola Ahmed Tinubu Ya Lashe Zaben Fidda Gwani Na Shugaban Kasa A Gombe Afrika
  • APC Ta Ayana Tsohon Gwamnan Bauchi M.A Abubakar A Matsayin Dan Takarar Gwamna Afrika

Kungiyar HPV A Jihar Gombe Ta Jagoranci Yaki Da Karuwar Cutar Daji
Published: April 5, 2026 at 10:15 AM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: April 6, 2026

Kungiyar HPV ta jihar Gombe ta shirya wani gangamin wayar da kan al’umma, inda ta hada ‘yan jarida, ma’aikatan lafiya, masana ilimi, shugabannin al’umma da sauran masu ruwa da tsaki domin tunkarar barazanar karuwar cutar daji a jihar.

Da yake jawabi a wajen taron, Farfesa Muhammad Manga ya bukaci mahalarta su kirkiro dabaru masu amfani domin hana yaduwar cutar daji, musamman cutar sankarar mahaifa, da kuma yadda za a magance sauran nau’o’in cutar a cikin al’umma.

Ya bayyana cewa an hada bangarori daban-daban cikin shirin ne da gangan, musamman mambobin Kungiyar ‘Yan Jarida ta Najeriya, domin inganta tattaunawa da gano hanyoyin magance matsalolin cutar daji.

Farfesa Manga ya yaba wa mahalarta taron bisa jajircewarsu, yana mai jaddada cewa ana iya warkar da cutar daji idan aka gano ta da wuri. Ya kuma bukaci jama’a da su gaggauta neman kulawar likita idan sun lura da wasu sauye-sauye ko alamomi da ba su saba ba, tare da karfafa musu gwiwa su yada wannan sakon wayar da kai a cikin al’ummominsu.

Sauran masu jawabi, ciki har da shugabar taron, Dakta Halima Usman Farouk, Farfesa Danladi Adamu Bojude da Ferfesa Aliyu Lawal na Asibitin Koyarwa na Tarayya da ke Gombe, da kuma shugabannin al’umma Musa Mustafa da Danimoh Mustafa, sun jaddada bukatar kara hadin gwiwa tsakanin ‘yan jarida, ma’aikatan lafiya da sauran masu ruwa da tsaki domin yakar cutar daji yadda ya kamata.

Sun bayyana wasu daga cikin nau’o’in cutar daji da suka fi yawaita a jihar da suka hada da na mama, huhu, mafitsara ta maza, mahaifa, hanta, ciki, pankiriyas, koda, mafitsara, fata, kwakwalwa, ovaries, mahaifa ta mata da kuma esophagus.

Masu jawabin sun bukaci jama’a da su rika anfani da ayyukan kiwon lafiya da ake da su ta hanyar yin gwaje-gwaje akai-akai. Wadanda aka gano suna dauke da cutar an shawarce su da su nemi magani da wuri, yayin da sauran kuma aka karfafa musu gwiwa su yi allurar rigakafi inda ya dace.

Kungiyar ta sake jaddada kudirinta na kara fadada shirye-shiryen wayar da kai da kuma inganta samun damar ayyukan rigakafi domin rage mace-macen da ke da alaka da cutar daji a Jihar Gombe.

Daga jihar Gombe ga Rahoton Wakilin GTA Hausa Amurka Ke Magana Aliyu Bala Gerengi

https://gtahausa.com/wp-content/uploads/2026/04/HPV-GOMBE.mp3
Afrika, Kiwon Lafiya, Labarai, Najeriya, Rumbun Hotuna

Post navigation

Previous Post: Majalisar Dokokin Kamaru Ta Amince Da Wasu Sauye Sauye
Next Post: Rundunar Sojin Najeriya Ta Kubutar Da Wasu Mutane 31 Da Aka Yi Garkuwa Dasu

Karin Labarai Masu Alaka

Rundunar Hadinkan Saudiya Tayi Ikirarin Mayar Da Martani Ga ‘Yan Aware Labarai
Guguwa Mai Karfi Ta Raunata Dubban Mutane A Madagascar Labarai
Rahoton MDD Yace An Kashe Fiye Da Farar 1000 A Sudan Labarai
Kasashen Turai: Bazamu Yarda Da Dokar Harajin Trump Ba Labarai
Majalisar Wakilai Tayi Allah Wadai Da Hare-Haren ‘Yan Bindiga A Gombe Labarai
Aikin Layin Dogon Kasar Uganda Zai Hade Kasar Da Tanzania Da Kwango Kimiya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Tsohuwar Jarumar Kannywood Wasila Ismail Ta Rasu
  • Za’a Fassara Hudubar Arfa Da Harshen Hausa
  • An Kamallah Jigilar Alhazain Najeriya Domin Hajjin 2026
  • Bola Ahmed Tinubu Ya Lashe Zaben Fidda Gwani Na Shugaban Kasa A Gombe
  • APC Ta Ayana Tsohon Gwamnan Bauchi M.A Abubakar A Matsayin Dan Takarar Gwamna

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • ‘Yan-Ta’adda Sun Kara Sace Mutane A Jihar Naija! Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Jamhuriyar Congo Zata Cigaba Da Fitar Da Ma’adanai Afrika
  • Tattalin Arzikin Kasar Bahrain Ya Bunkasa Sakamakon Ruruwar Masu Yawon Bude Ido Labarai
  • Shugaba Bola Tinubu Ya Saka Hannu A Dokar Zabe Najeriya
  • Rundunar Tsaron Haɗin Gwiwa Ta Arewa Maso Gabas Ta Kashe Fiye Da ‘Yan Ta’adda 438 Labarai
  • Wani Jirgi Yayi Saukar Angulu Ba Shiri Najeriya
  • Aikin Layin Dogon Kasar Uganda Zai Hade Kasar Da Tanzania Da Kwango Kimiya
  • Shugaban Amurka Yace Sojojin Amurka Dana Iran Sunyi Taho Mugama Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.