Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Rundunar ‘Yan Sandan Gombe Ta Kuɓutar da Yaro Daga Hannun Masu Garkuwa Afrika
  • Tinubu Ya Buɗe Katafaren Kamfanin Sarrafa Lithium Domin Bunƙasa Tattalin Arziki Afrika
  • Sojoji Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 1,597, Sun Ceto Mutane 1,516 – DHQ Afrika
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u Afrika
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa Afrika

Gobara Ta Tashi A Makarantar Koyon Jinyar Dabbobi Dake Jihar Kano
Published: January 22, 2026 at 5:51 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Wata gobara da ta tashi a ranar Litinin ta ƙone ajujuwan karatu 34 a wata makarantar kiwon lafiyar dabbobi da ke karamar hukumar Kabo a jihar Kano.

A cewar wata sanarwa da jami’in hulɗa da jama’a na hukumar kashe gobara ta ta Jihar Kano, ACFO Saminu Yusif Abdullahi, ya fitar, ya ce lamarin ya faru da misalin ƙarfe 2:53 na rana.

Sanarwar ta ce dakin kula da gobara na hukumar ya karɓi kiran taimako daga wani Jamilu Abubakar, wanda ya ba da rahoton tashin gobara a cikin makarantar. Nan da nan aka tura ma’aikatan kashe gobara daga tashar Rijiyar Zaki zuwa wurin da lamarin ya faru.

“Da suka iso wurin, ma’aikatanmu sun gano wani ginin bene na ƙasa mai fadin ƙafa 500 da tsayin ƙafa 500, da ake amfani da shi a matsayin wajen kiwon lafiyar dabbobi, yana ƙonewa cikin wuta,” in ji sanarwar.

Sanarwar ta ƙara da cewa dakuna 16 sun lalace sosai, yayin da wasu 18 suka samu lalacewar ɓangare-ɓangare saboda gobarar.

Sai dai an samu nasarar dakile wutar, inda aka hana ta yaɗuwa zuwa sauran dakuna da ofisoshi a cikin cibiyar.

“An tura motar kashe gobara guda ɗaya daga tashar Rijiyar Zaki don dakile lamarin, in ji sanarwar, wadda ta danganta nasarar aikin da saurin martanin ma’aikatan kashe gobara.

Ba a samu rahoton mutuwar kowa ba a lokacin da ake rubuta wannan rahoto, yayin da ba a bayyana musabbabin gobarar ba.

Najeriya

Post navigation

Previous Post: Shugaba Trump Ya Janye Karbar Kudin Fito Daga Wasu Kasashen Turai
Next Post: Bassirou: Tawagar Senegal Zasu Samu Kyautar Kudi Da Filaye Sakamakon Nasarar Da sukayi AFCON 2025

Karin Labarai Masu Alaka

Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Gwamnatin Kano Ta Rufe Gidajen Bukukuwa Da Shakatawa Labarai
Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari Afrika
Sabon Babin Tsaro A Najeriya: Gombe Ta Fito Da Tsarin Smart Security Na Farko Afrika
Farfesa Inuwa Ja’afaru Yakarbi Ragamar Shugabancin Jami’ar Kashere Labarai
An Samu Bullar Cutar COVID 19 A Najeriya Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Rundunar ‘Yan Sandan Gombe Ta Kuɓutar da Yaro Daga Hannun Masu Garkuwa
  • Tinubu Ya Buɗe Katafaren Kamfanin Sarrafa Lithium Domin Bunƙasa Tattalin Arziki
  • Sojoji Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 1,597, Sun Ceto Mutane 1,516 – DHQ
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Kungiyar ECOWAS Ta Koka Game Da Yawan Juyin Mulki A Kasashen Afirka Afrika
  • Shugaban Amurka Zai Sake Aika Jirgin Yaki Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Amurka Ta Kulla Yarjejeniya Da Kasashe Hudu Domin Inganta Kiwon Lafiya Labarai
  • Za’ayi Auren Zawarawa Dubu Uku A Kano Afrika
  • Trump Yayi Kira Ga ‘Yan Ƙasar Iran Su Ci Gaba Da Zanga Zanga Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Sanda A Tsibirin Bahamas Sun kama Mijin Wata Ba Amurkiya Amurka
  • Bayan Ya Ziyarci Kwankwaso Gawuna Zai Karbi Katin ADC Afrika
  • Shugaban Kasar Najeriya Ya Gabatar Da Kudi Fiye Da Naira Triliyan 58 A Matsayin Kasafin 2026 Najeriya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.