Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Gobara Ta Tashi A Makarantar Koyon Jinyar Dabbobi Dake Jihar Kano
Published: January 22, 2026 at 5:51 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Wata gobara da ta tashi a ranar Litinin ta ƙone ajujuwan karatu 34 a wata makarantar kiwon lafiyar dabbobi da ke karamar hukumar Kabo a jihar Kano.

A cewar wata sanarwa da jami’in hulɗa da jama’a na hukumar kashe gobara ta ta Jihar Kano, ACFO Saminu Yusif Abdullahi, ya fitar, ya ce lamarin ya faru da misalin ƙarfe 2:53 na rana.

Sanarwar ta ce dakin kula da gobara na hukumar ya karɓi kiran taimako daga wani Jamilu Abubakar, wanda ya ba da rahoton tashin gobara a cikin makarantar. Nan da nan aka tura ma’aikatan kashe gobara daga tashar Rijiyar Zaki zuwa wurin da lamarin ya faru.

“Da suka iso wurin, ma’aikatanmu sun gano wani ginin bene na ƙasa mai fadin ƙafa 500 da tsayin ƙafa 500, da ake amfani da shi a matsayin wajen kiwon lafiyar dabbobi, yana ƙonewa cikin wuta,” in ji sanarwar.

Sanarwar ta ƙara da cewa dakuna 16 sun lalace sosai, yayin da wasu 18 suka samu lalacewar ɓangare-ɓangare saboda gobarar.

Sai dai an samu nasarar dakile wutar, inda aka hana ta yaɗuwa zuwa sauran dakuna da ofisoshi a cikin cibiyar.

“An tura motar kashe gobara guda ɗaya daga tashar Rijiyar Zaki don dakile lamarin, in ji sanarwar, wadda ta danganta nasarar aikin da saurin martanin ma’aikatan kashe gobara.

Ba a samu rahoton mutuwar kowa ba a lokacin da ake rubuta wannan rahoto, yayin da ba a bayyana musabbabin gobarar ba.

Najeriya

Post navigation

Previous Post: Shugaba Trump Ya Janye Karbar Kudin Fito Daga Wasu Kasashen Turai
Next Post: Bassirou: Tawagar Senegal Zasu Samu Kyautar Kudi Da Filaye Sakamakon Nasarar Da sukayi AFCON 2025

Karin Labarai Masu Alaka

Gwamnatin Gombe Ta Aza Tubalin Gina Sakatariyar Gundumomin Cigaba (LCDAs) Labarai
Ganduje: Mun Janye Shirin Kafa Hisbah Mai Zaman Kanta A Kano Najeriya
Akwai Alamar Shawarwari Tsakanin Amurka Da Turai Zai Kawo Karshen Yakin Rasha Amurka
Wata Tankar Mai Ta Kife A Apapa Legas Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Jihar Gombe Ta Saka Hannu Kan Yarjejeniya Da Kamfanonin Tunisiya Kimiya
Kungiyar Mata Manoma A Najeriya Ta Raba Kyautar Abinci A Gombe Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Yakin Gabas Ta Tsakiya Ya Kawo Cikas Ga Cinikin Nama A Kenya
  • Sabon Jagoran Addinin Iran Mojtaba Khameni Yaji Rauni Kuma Ya Nakasa
  • Shugaba Trump Yace Amurka Takai Hari Kharg Tsibiri a Kasar Iran
  • MDD: Fiye Da Farar Hula Metan 200 Suka Mutu A Sudan
  • Jami’ai A Afirka Sunce Tashin Farashin Mai Kalubale Ne Ga Tattalin Arziki

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Hukumar Tsaron Civil Defence A Gombe Ta Samar Da Jami’ai Don Tabbatar Da Tsaro A Bukukuwan Karshen Shekara Labarai
  • Nada Jakadu Da Tinubu Yayi Sako Ne Ga ‘Yan-Arewa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • An Samu Kaburbura Biyu Dauke Da Gawarwaki 173 A Kasar Kwango Afrika
  • FIFA Ta Yi Wa Malaysia Kaca-kaca Wasanni
  • Wakilan Majalisar Dokokin Phillipines Suna Yunkurin Tsige Shugaban Kasar Afrika
  • Sarkin Musulmi Yayi Magana Game Da Matsalar Tsaron Kasar Tsaro
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Yagana Da Shugaban Sa’ido Akan Nukiliya Afrika
  • Gwamna Fubara Ya Koma Jam’iyar APC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.