A jiya Alhamis, jami’an kasar Faransa sun musanta ware kasar Afirka ta Kudu daga jerin kasashen da aka gayyata zuwa taron shugabannin kasashen G7 a watan Yuni saboda matsi daga fadar Washington, suna mai cewa an gayyaci kasar Kenya ne maimakon ta, kafin zuwa shugaban Faransa Emmanuel Macron nan gaba cikin shekarar nan.
Faransa ta sanar a baya cewa zata karbi bakuncin shugabannin India, Koriya ta Kudu, Brazil da Kenya a taron da za’a gudanar a Evian les Bain.
Kasar Afirka ta Kudu, wadda ta saba halartar taron na G7, tace ofishin jakadancin Faransa a Pretoria ya sanarwa da gwamnatin kasar shawara da aka yanke kusan makonni biyu da suka wuce, suna me cewa Amurka tayi barazanar kin halatar taron idan aka gayyaci Afirka ta Kudu.
Amma da aka tuntubi Faransa ko an ware Afirka ta Kudu ne bisa bukatar Amurka, wani jami’in Faransa ya ce ba haka bane, kawai Faransa ta yanke shawarar gayyatar Kenya a wannan lokacin.


