Gwamnan jihar Gombe, Alhaji Muhammadu Inuwa Yahaya, ya samu muƙamin Kodinetan Tattara Masu Ruwa da Tsaki na Yankin Arewa Maso Gabas a sabon Kwamitin Yaƙin Neman Zaɓen Shugaban Ƙasar Najeriya na Jam’iyyar APC na shekarar 2027.
An bayyana naɗin Gwamna Inuwa Yahaya ne cikin jerin sunayen mambobin kwamitin da aka fitar ranar Asabar, 22 ga Agustan 2026, tare da naɗe-naɗen sauran mambobin kwamitin.
A sabon matsayinsa, Gwamna Inuwa Yahaya zai jagoranci hulɗa da tattara muhimman masu ruwa da tsaki na APC a jihohi shida na yankin Arewa Maso Gabas, gabanin zaɓen shugaban ƙasa na 2027.
Shugaban Ƙasar Najeriya Bola Ahmed Tinubu ne ke jagorantar Kwamitin Yaƙin Neman Zaɓen Shugaban Ƙasar, yayin da Mataimakin Shugaban Ƙasa Kashim Shettima da Shugaban Jam’iyyar APC na Ƙasa, Farfesa Nentawe Yilwatda, ke matsayin mataimakan shugabanni.
Tsohon Gwamnan Jihar Zamfara, Sanata Abdul’aziz Yari, shi ne Darakta-Janar na kwamitin, yayin da Gwamnan Jihar Imo, Hope Uzodimma, ke matsayin Sakataren kwamitin.
Naɗin Gwamna Inuwa Yahaya na ƙara nuna muhimmiyar rawar da yake takawa a cikin APC, musamman wajen ƙarfafa haɗin kan jam’iyya, hulɗa da masu ruwa da tsaki da kuma tattara magoya baya a matakin ƙasa a yankin Arewa Maso Gabas.
Gwamna Inuwa Yahaya, wanda ke wa’adi na biyu a matsayin Gwamnan Jihar Gombe, kuma ɗan takarar APC na Majalisar Dattawa mai wakiltar Gombe ta Arewa, ƙwararren ɗan siyasa ne mai gogewa a harkokin tafiyar da jam’iyya, hulɗa da masu ruwa da tsaki da kuma tattara jama’a.
Wannan sabon naɗi ya ƙara faɗaɗa nauyin da ke kansa a tsarin tattara magoya bayan APC. Kwanan nan Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya naɗa shi Sakataren Renewed Hope Ambassadors, inda aka ɗora masa alhakin hulɗa da jama’a da kuma tattara goyon baya ga jam’iyya.
Saboda kyakkyawar alaƙarsa da ’yan siyasa da masu ruwa da tsaki, da kuma fahimtarsa kan siyasar yankin Arewa Maso Gabas, Gwamna Inuwa Yahaya na da damar amfani da gogewarsa wajen ƙara ƙarfafa goyon bayan Shugaba Tinubu da jam’iyyar APC a yankin.


