Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai Afrika
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari Afrika
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe Afrika
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS Afrika
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe Afrika

Babban Hafsan Tsaron Najeriya Ya Gargadi Masu Tayar Da Hankali
Published: January 24, 2026 at 9:24 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Babban Hafsan Sojin Ƙasarln Najeriya, Laftanar Janar Waidi Shaibu, ya yi gargaɗi mai tsanani ga masu aikata laifuka da ke tayar da hankalin al’umma a faɗin ƙasar, inda ya ce za su fuskanci ƙarfin sojoji matuƙar ba su tuba daga munanan ayyukansu ba.

Fiye da sojojin musamman dubu ɗaya (1,000) ne aka ƙara tura wa fagen yaƙi domin ƙarfafa ayyukan tsaron cikin gida da ake gudanarwa a sassa daban-daban na ƙasar.

Babban Hafsan Sojin ya bayyana hakan ne yayin bikin kammala atisayen Exercise Restore Hope 9 da aka gudanar a sansanin rundunar sojin Najeriya da ke Kachia.

Ya jaddada cewa rundunar sojin ƙasa za ta ci gaba da tinkarar duk wani ɓangare na masu tada fitina, inda ya ce duk masu aikata laifi za su gamu da ƙarfin da za su iya jurewa, har sai sun daina munanan ayyukansu kuma sun tuba.

Ya kuma tabbatar wa ‘yan Najeriya cewa rundunar sojin ƙasa za ta ci gaba da jajircewa wajen kare rayuka da dukiyoyin jama’a.

Najeriya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Gwamna Ododo Ya Gargadi Sarakunan Gargajiya
Next Post: Najeriya Da Amurka Sun Amince Su Haɗa Kai Don Inganta ’Yancin Addini Da ƙarfafa Tsaro A Nijeriya

Karin Labarai Masu Alaka

An Kusa Kawo Karshen Matsalolin Tsaro A Jihar Filato Afrika
Shugaba Tinubu Ya Taya Murtala Garo Murnar Zama Mataimakin Gwamnan Kano Labarai
Hukumar NAHCON Ta Bude Asibiti A Madina Afrika
Iran Zata Mayarwa Amurka Martani Amurka
Babban Sufeton ‘Yan Sandan Najeriya Ya Sauka A Mukaminsa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Shugabannin Kasar Australia Sun Bukaci ‘Yan Kasar Suyi Zanga Zanga Cikin Lumana Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • ‘Yan Gudun Hijira A Kasar Libya Suna Fuskantar Cin Zarafi Afrika
  • Gwamnatin Bauchi: Ta Kaddamar Da Kwamitin Ma’adanai Labarai
  • ‘Yan Ta’adda Sun Tarwatsa Wani Kauye A Jihar Sakkwato Tsaro
  • Ana Cigaba Da Ceto Masunta Daga Ruwa A Ghana Labarai
  • Nuhu Ribadu Ya Mika Dalibai 100 da Aka Ceto Ga Gwamnatin Jihar Neja Labarai
  • An Garkame Wani Babban Soja A Kasar Australiya Afrika
  • Rasha Ta Yiwa Amurka Tayin Daina Bada Bayanan Sirri Afrika
  • Shugaba Trump Yace Amurka Takai Hari Kharg Tsibiri a Kasar Iran Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.