Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojoji Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 1,597, Sun Ceto Mutane 1,516 – DHQ Afrika
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u Afrika
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa Afrika
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa Afrika

Suvr Jahun: Ya Kamata Obasanjo Ya Bar Al’umar Ƙasa Su Fito Da Wadda Suke So 2027
Published: January 21, 2026 at 9:00 AM | By: Bala Hassan

An ja hankalin tsohon Shugaban Kasar Najeriya Olushegun Obasanjo kan wasu kalaman kiyayya da yake yi wa Atiku Abubakar

Suvr. Lawal Jahun Chiroman Galadiman Bauchi tsohon Malamin Kwalejin kimiya da fasaha na gwamnatin tarayyar Najeriya dake Bauchi shine yayi wannan kira ga Obasanjo, a wata hira da yayi da GTA Hausa.

Lawal yace Obasanjo yanzu a Najeriya shi uba ne saboda haka kowa nasane bai da ce da wasu kalamai na nuna cewa Atiku Abubakar bai cancanci zama Shugaban ƙasa ba.

Mun san cewa Atiku yayi mataimaki wa Obasanjo na tsawon shekaru takwas duk da cewa an san sun kare dutse a hannun riga amman Atiku ya taimaki Obasanjo a lokacin da ya ke niman tazarce, shi ya shawo kan Gwamnoni musan na arewa yace suyi hakuri su sake zaban Obasanjo karo na biyu

An sani cewar duk shugaba yana da yadda za’a yaba masa bisa wasu ayyukan cigaba da ya kawo a kwai kuma yadda ya gaza saboda shi dan adam ne tara yake bai cika goma ba.

A lokacin Obasanjo cigaba da aka samu a shi ne bangaren tsaro da kuma yaki da yunwa, wannan kowa yasani amman a inda yagaza shine ya halarta wa gwamnonin jihohi su karbi kudin kananan Hukumomin wadda ya jawo kananan Hukumomin suka fita hayyacinsu a yanzu haka.

Matsalolin da aka samu tsakanin tsohon mataimakin shugaban ƙasa Atiku da Obasanjo ai shi Atiku yayi tattaki har zuwa gidan gonan Obasanjo domin su dai dai ta amman Obasanjo yaki ” Inji Suvr Lawal.

Amman abunda muka fahinta shine Obasanjo yana kin Atiku ne saboda yana tsoron kar ya tona masa wani asiri tunda sunyi aiki tare ya san wasu sirrinsa, ko kuma ya na tsoron kar ya rama abunda ya masa duk da bama son a yi mulki na ramukon gayya.

Saboda haka idan Obasanjo bazai goyi bayan Atiku ba to ya bari al’umar ƙasa su zabi wadda suke so domin su za’a mulka.

Lawal ya kara da cewa yanzu a Najeriya babu wani kamar tsohon mataimakin shugaban ƙasa Atiku Abubakar in dai batun siyasa ne haka kuma a jihar Bauchi Baba kamar Air vice Marshal Sadiq Baba Abubakar ritaya.

https://gtahausa.com/wp-content/uploads/2026/01/SUVR-LAWAL-JAHUN.mp3
Najeriya

Post navigation

Previous Post: Menene Illar Yada Labaran Karya A Kafofin Sada Zumunta Na Zamani
Next Post: Sojojin Najeriya Sun Kwato Mutane Daga Hannun Masu Garkuwa

Karin Labarai Masu Alaka

Rundunar Operation Endurance Peace Ta Gano Wajen Kera Makamai A Jihar Filato Afrika
Jami’ar Tarayya A Gombe Ta Karyata Harin ‘Yan Bindiga Najeriya
Najeriya Zata Kara Mai Da Take Hakowa Afrika
Tsohon Minista Ngige Ya Shiga Komar EFCC Najeriya
Shugaba Tinubu Ya Yabawa Dakarun Tsaro Bisa Ceto Matar Marigayi Janar Rabe Afrika
An Kama Wani Da Abubuwan Fashewa A Zamfara Najeriya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojoji Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 1,597, Sun Ceto Mutane 1,516 – DHQ
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Babban Sakataren MDD Yayi Allah Wadai Da Matakin Soja A Gabas Ta Tsakiya Afrika
  • ‘Yan Sandan Habasha Sun Kama Dubban Albarusai Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ana Cigaba Da Samun Hare Hare Da Jiragen Marasa Matuki A Sudan Labarai
  • Gwamnan Jihar Gombe Ya Umurci A Rufe Makarantu Labarai
  • Gobara Ta Tashi A Makarantar Koyon Jinyar Dabbobi Dake Jihar Kano Najeriya
  • Akwai Shakku Akan Sanin Wacce Kungiyar Kwallon Kaface Zata Lashe Gasar Kofin Afirka Da Akeyi A Morocco Nishadi
  • FIFA, Ta Raba Jaddawalin Rukuni Na Gasar Kofin Duniya 2026. Wasanni
  • Nan Gaba Kadan Kwallon Badminton Zata Samu Karbuwa Kamar Kwallon Kafa A Duniya Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.