Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u Afrika
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa Afrika
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa Afrika
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed Afrika

‘Yan Sandan Habasha Sun Kama Dubban Albarusai
Published: January 15, 2026 at 9:27 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

‘Yan sanda a Habasha ko Ethiopia sunce sun kama dubban albarusai da Eritrea ta aikawa ‘yan tawaye a yankin Amhara, zargin da Eritean tayi watsi da shi a zaman kariya da Ethiopia ta zuka da nufin kafa hujjar ta afka yaki.

Zargin da rundunar ‘Yansandan kasar Ethiopia tayi ya zafafa rikici tsakanin kasashen biyu, da suka jima suna gaba da juna, amma suka kulla yarjejeniyar zaman lafiya a 2018, wadda tuni sabbin barazana tsakanin kasashen biyu yake maye gurbinta.

A cikin sanarwar data bayar a daren ranar Laraba, rundunar ‘Yan sandan a habashan tace ta kama albarusai dubu 56,000, ta kama mutane biyu a yankin Amhara cikin makon nan, yankin da kungiyar ‘yan tawaye da ake kira Fano take kaddamar da hare hare da turjiya tun a shekarar 2023.

Ministan yada labarai a Eritrea Yemane Gebremeskel, ya fadawa kamfain dillancin labarai na Reuters cewa, jam’iyyar PP ta PM Abiy Ahmed, tana neman wata hujjar da zata fake dashi domin ta kai farmaki.

Tunda a farkon wannan mako a hira da yayi a kafofin yada labaran Erirea, shugaban kasar Isaias Afwerki, yace jam’iyyar PP a Habasha ta ayyana yaki kan kasarsa.

Kasashen biyu sun gwabza yaki kan rikicin kan iyaka rikici da ya barke a shekara ta 1998, shekaru biyar bayan da Eritrea ta sami ‘yancin kai daga kasar Habasha ko Ethiopia.

Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Ghana Tayi Watsi Da Yarjejeniya Akan Hakar Ma’adanai
Next Post: Shugaba Trump Yayi Barazanar Tura Sojoji Ga Masu Zanga Zanga

Karin Labarai Masu Alaka

Jirage Marasa Matuka Sun Kaiwa Jiragen Ruwan Mai Hari A Gulf Afrika
Mutane 27 Sun Rasa Rayukan Su A Najeriya Afrika
Shugaba Trump Yace Amurka Zata Janye Yaki Da Iran Afrika
Jama’a A Yankin Gulf Sun Bukaci Dakatar Da Hare Hare Daga Washington Afrika
Indonesia Zata Kafafa Rundunar Kiyaye Zaman Lafiya A Gaza Labarai
Amurka Ta Yi Juyin Mulki A Kasar Venezuela Amurka

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Hafsan Sojin Najeriya: Samar Da Sabbin Wajen Horas Da Sojoji Zai Inganta Tsaro Tsaro
  • Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf Ya Gana Da Shugaba Tinubu Siyasa
  • Kungiyar Kwallon Mata Sun Tsallaka Iyakar Turkiyya Zuwa Iran Afrika
  • Umar Ya Lashe Kyautar Gwarzon ‘Dan-Wasa Na 2025 Wasanni
  • Kasar China Ta Sauka Daga Ragamar Bada Bashi Labarai
  • Gwamnatin Gombe Ta Raba Naira Miliyan 14 Ga Iyalen ‘Yan Jaridan Da Suka Rasu Najeriya
  • Kotu A Kasar Tunisiya Ta Daure Wani Babban Dan Kasuwa Da Wasu ‘Yan Majalisa Afrika
  • Al’ummar Jihar Nasarawa Suna Cecekuce Bisa Tsaida Aliyu Wadada Takarar Gwamna Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.