Donald Trump yace Amurka na tunanin janye yaki da Iran, yayin da Iran da Isra’ila ke ci gaba da musayar hare-hare a ranar Asabar. Tasoshin yada labarai a Iran sun ce an kai hari cibiyar makamashin nukiliyan ta na Nantaz.
A wani sako da ya wallafa a kafar sada zumunta, Trump yace Amurka na gab da cika burin ta, amma ya dage kan cewa sai sauran kasashe sun shige gaba wajen sha’anin mashigin ruwa na Hormuz, wanda cigaba da rufe shi ya ke kawo cikas ga samar da makamashi a duniya.
Trump ya nuna alamar cewa yaki zai tsagaita, tun da an kau da barazanar da Iran ke da shi, a yayin da kuma sojin ruwan Amurka da kayan yaki suka durfafi yankin.


