Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Jami’an ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayi Afrika
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai Afrika
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari Afrika
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe Afrika
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS Afrika

NLC Ta Yabawa Gwamnan Gombe Inuwa Yahaya
Published: December 14, 2025 at 2:37 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Shugaban Ƙungiyar Ƙwadago ta Najeriya (NLC), Kwamared Joe Ajaero, ya yabawa Gwamnan jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, bisa irin kulawa da tabbatar da jin daɗin ma’aikata a jihar.

Ajaero ya bayyana hakan yayin wani taron da ya gudana, inda ya ce ko da yake ƙungiyar ba ta cika yawan yabon gwamnoni ba, amma Gwamna Inuwa Yahaya ya cancanci yabo bisa irin yadda yake baiwa ma’aikata muhimmanci da kuma cika alƙawurra.

Saboda haka, NLC ta karrama Gwamna Inuwa da lambar yabo ta “Gwamna Mai Ƙaunar Ma’aikata”, a matsayin wanda ke da kyakkyawar dangantaka da ma’aikatansa tare da ɗaukar walwalarsu a matsayin fifiko.

Wannan karramawa na zuwa ne a daidai lokacin da gwamnatin Gombe ke ci gaba da aiwatar da manufofi da tsare-tsare da suka shafi ci gaban ma’aikata da inganta rayuwar su kamar aiwatar da mafi karancin albashi da kuma aza tubalin gida ofishin sakatariyar kwadago.

Najeriya

Post navigation

Previous Post: Jirgin Sama Ya Fadi A Kano
Next Post: Gwamna Kefas Na Jihar Taraba Ya Karbi Shaidar Jam’iyar APC

Karin Labarai Masu Alaka

Shugaban Kasar Najeriya Ya Gabatar Da Kudi Fiye Da Naira Triliyan 58 A Matsayin Kasafin 2026 Najeriya
Lauya Bala: Tabbas Kotu Zata Soke Zaben Shugaban PDP, Turaki Najeriya
Shugaban Ƙasar Koriya Ta Arewa Ya Halarci Gwajin Makami Mai Linzamin Kasar Labarai
Jam’iyyar APC Ta Rantsar Da Sabbin Shugabanni a Jihar Neja Labarai
Motar Kungiyar Kwallon Kafar Bayelsa United Ta Yi Hatsari Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Sabunta Manhajar Ilimi A Duk Matakai Nasara Ce! Najeriya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jami’an ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayi
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Domin Inganta Tsaro Najeriya Ta Sayi Jiragen Yaki A Kasar Italiya Tsaro
  • Abba Kabir: Zamu Samar da Jirage Marasa Matuka A Kano Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Barcelona na hangen Enrique Ko Arteta Wasanni
  • Gwamnatin Tarayya Tana Neman Kudi Domin Aiwatar Da Kasafin Kudin 2026 Najeriya
  • Rahoton MDD Yace An Kashe Fiye Da Farar 1000 A Sudan Labarai
  • Dakarun Gwamnatin Kasar Sham Tayi Mamaya Zuwa Gabashin Kasar Labarai
  • Sojojin Faransa Sun Karyata Zargin Bobi Wine Labarai
  • Motsepe, Daga 2028 AFCON Zata Sauya Daga Shekaru Biyu Zuwa Hudu Wasanni
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.