Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Ƙungiyoyin Ƙwadago Sun Ce Albashin ₦70,000 Ya Gaza Biyan Bukatun Ma’aikata Afrika
  • NUJ Gombe Ta Ƙarfafa Bin Ɗa’a A Aikin Jarida, Ta Kaddamar Da Kwamitin Ladabtarwa Afrika
  • Hukumar UBRBDA Ta Fara Raba Kayan Noma A Gombe, Yobe Da Borno Amurka
  • Masu Ruwa Da Tsaki Sun Buƙaci Ƙarin Tallafi Ga Iyaye Mata Masu Shayarwa A Gombe Afrika
  • Rundunar ‘Yan Sandan Gombe Ta Yi Gargaɗi Ga Masu Karya Dokokin Hanya Afrika

NLC Ta Yabawa Gwamnan Gombe Inuwa Yahaya
Published: December 14, 2025 at 2:37 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Shugaban Ƙungiyar Ƙwadago ta Najeriya (NLC), Kwamared Joe Ajaero, ya yabawa Gwamnan jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, bisa irin kulawa da tabbatar da jin daɗin ma’aikata a jihar.

Ajaero ya bayyana hakan yayin wani taron da ya gudana, inda ya ce ko da yake ƙungiyar ba ta cika yawan yabon gwamnoni ba, amma Gwamna Inuwa Yahaya ya cancanci yabo bisa irin yadda yake baiwa ma’aikata muhimmanci da kuma cika alƙawurra.

Saboda haka, NLC ta karrama Gwamna Inuwa da lambar yabo ta “Gwamna Mai Ƙaunar Ma’aikata”, a matsayin wanda ke da kyakkyawar dangantaka da ma’aikatansa tare da ɗaukar walwalarsu a matsayin fifiko.

Wannan karramawa na zuwa ne a daidai lokacin da gwamnatin Gombe ke ci gaba da aiwatar da manufofi da tsare-tsare da suka shafi ci gaban ma’aikata da inganta rayuwar su kamar aiwatar da mafi karancin albashi da kuma aza tubalin gida ofishin sakatariyar kwadago.

Najeriya

Post navigation

Previous Post: Jirgin Sama Ya Fadi A Kano
Next Post: Gwamna Kefas Na Jihar Taraba Ya Karbi Shaidar Jam’iyar APC

Karin Labarai Masu Alaka

An Kama Wani Da Abubuwan Fashewa A Zamfara Najeriya
Zargin Fitar Da Bayanan Masu Zabe A Najeriya Afrika
Sabuwar Dama Ga Masu Zaɓe: INEC Ta Tsawaita CVR Zuwa Ƙarshen Yuli Afrika
‘Yan Jarida Sunyi Mummunan Hatsari A Bauchi Labarai
Ana Cigaba Da Bincike Game Da Mutuwar Matar Da Likita Ya Manta Almakashi A Cikinta A Kano Najeriya
Amurka Ta Nuna Damuwa Kan Matsalar ‘Yan Gudun Hijira A Najeriya Najeriya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Ƙungiyoyin Ƙwadago Sun Ce Albashin ₦70,000 Ya Gaza Biyan Bukatun Ma’aikata
  • NUJ Gombe Ta Ƙarfafa Bin Ɗa’a A Aikin Jarida, Ta Kaddamar Da Kwamitin Ladabtarwa
  • Hukumar UBRBDA Ta Fara Raba Kayan Noma A Gombe, Yobe Da Borno
  • Masu Ruwa Da Tsaki Sun Buƙaci Ƙarin Tallafi Ga Iyaye Mata Masu Shayarwa A Gombe
  • Rundunar ‘Yan Sandan Gombe Ta Yi Gargaɗi Ga Masu Karya Dokokin Hanya

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • ‘Yan Agajin Izalar Jos Sunyi Hatsari Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Pantami Ya Bayyana Dalilin Mayar Da Zaben Sa Abuja Afrika
  • Shugaba Tinubu: Naji Dadin Sako Daliban Neja Da Aka Sace Labarai
  • Kasar Rasha Ta Zargi Ukraine Da Kai Hari Gidan Shugaban Rasha Amurka
  • An Gudanar Da Zanga-Zanga A Guinea-Bissau Afrika
  • Kwamitin Aikin Hajjin Najeriya Ya Shigar Da Korafi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamna Inuwa Yahaya Ya Rantsar Da Sabon Shugaban Ma’aikatan Jiha da Kwamishinoni 23 Afrika
  • TIC Dutse Ta Nemi Ƙarin Tallafin Gwamnatin Jigawa Don Faɗaɗa Ayyukanta Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.