Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai Afrika
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari Afrika
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe Afrika
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS Afrika
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe Afrika

Kungiyar Gwamnonin Arewacin Najeriya Tayi Kakkausar Lafazi Game Da Harin Maiduguri
Published: March 17, 2026 at 10:36 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Kungiyar Gwamnonin Arewacin Najeriya, karkashin jagorancin Gwamnan jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, ta yi Ala-wadai da harin bama-bamai da ya auku a birnin Maiduguri na jihar Borno, wanda ya yi sanadin asarar rayuka da jikkatar mutane da dama.

A cikin wata sanarwa da aka fitar ta bakin shugaban kungiyar, Inuwa Yahaya, gwamnonin sun bayyana harin a matsayin abin takaici da kuma babbar barazana ga zaman lafiya da tsaron al’umma a yankin Arewa maso Gabas. Sun jajantawa gwamnatin jihar Borno da iyalan wadanda abin ya shafa, tare da addu’ar Allah ya jikansu da rahama, ya kuma bai wa wadanda suka jikkata lafiya.

Kungiyar ta bukaci hukumomin tsaro da su kara kaimi wajen bincike domin gano wadanda ke da hannu a harin, tare da tabbatar da an hukunta su bisa doka.

Haka zalika, sun jaddada bukatar daukar matakan gaggawa domin kawo karshen irin wadannan hare-hare, tare da karfafa tsaro musamman a wuraren taruwar jama’a.

Gwamnonin sun kuma yi kira ga gwamnatin tarayya da ta kara tallafawa rundunonin tsaro da kayan aiki na zamani, da kuma inganta hadin gwiwa tsakanin jami’an tsaro da al’umma domin dakile ayyukan ta’addanci a fadin yankin.

Afrika, Labarai, Najeriya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Tinubu, Akpabio da Ministoci 9 Zasu Tafi Ƙasar Birtaniya
Next Post: Gwamnatin Najeriya Ta Ayyana Ranakun Hutun Sallar Azumi

Karin Labarai Masu Alaka

Anfara Gangamin Kafa Dokoki Masu Tsanani Ga ‘Yan Luwadi A Senegal Afrika
Shugaba Trump Ya Bukaci A Cigaba Da Zanga Zanga A Iran Labarai
Gwamnatin Jihar Filato Ta Sauke Hakimin Mushere Afrika
‘Yan Ta’adda Sun Hallaka Malaman Makaranta A Tilabery Afrika
Tsofin Shugabanin Kasa Sun Karbi Bakoncin Hafsan Sojin Najeriya Tsaro
Hukumar ‘Yan Sanda Ta Bukaci Jama’ar Jos Ta Arewa Su Rika Bin Doka Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • ECOWAS Zata Kafa Rundunar Yaki Da Rashin Tsaro Afrika
  • An Kai Hari Da Jirgi Mara Matuki A Kusa Da Matatar Mai Din Kasar Sundan Afrika
  • Kayan Jinya Da Ayyukan Kiwon Lafiya Suna Barazanar Karewa A Sudan Kiwon Lafiya
  • Amurka Zata Bada Gudunwa Ga Masu Zanga-Zanga A Iran Sauran Duniya
  • Amurka Da Isra’ila Sunkai Hari Kan Iran Amurka
  • Babban Bankin Najeriya Ya Rage Kudin Ruwa Da Kashi Daya Cikin Dari Labarai
  • Hukumar Hasashen Kasuwanci Na Zargin Saida Bayanan Sirri Amurka
  • Ana Tuhumar Dan Shugaba Robert Magabe Da Kisan Kai Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.