Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai Afrika
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari Afrika
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe Afrika
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS Afrika
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe Afrika

Kayan Jinya Da Ayyukan Kiwon Lafiya Suna Barazanar Karewa A Sudan
Published: March 18, 2026 at 8:31 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

A Sudan nan da mako biyu kayan jinya da ayyukan kiwon lafiya a cibiyoyin kiwon lafiyar kasar za su kare, sakamakon rikicin da ake yi a gabas ta tsakiya wadda ya janyo tsaiko na jigilar kayan jinya, muddin ba sake hanyar da aka saba bi ba, kamar yadda kungiyar tallafawa yara da ake kira Save the Chldren ta fada.

Yakin da Amurka da Isra’ila suka kaddamar kan Iran wadda yake kara bazuwa ya girgiza hanyoyin zirga zirga da jigila, saboda rufe sararin samaniyar da wasu kasashe suka yi, da kuma dakatar da jigilar kaya ta mashigin ruwan Hormuz.

Akwai magunguna da kayan Kiwon lafiya na kudi samada dala dubu dari shida wadanda ahalin yanzu suka makale a Dubai inji kungiyar da take ayyukan jinkai.

Kimanin cibiyoyin kiwon lafiya na gwamnatin Sudan 90, da suke kula da lafiyar mutane kusan dubu dari hudu sun dogara ne kan wannan kungiyar wajen samarda magunguna da sauran kayan jinya, kuma babu wata kafa a cikin kasar da zata iya samarda haka, inji wani jami’in kungiyar ta Save the Children.

Rikicin da ake yi a Sudan, tsawon shekaru uku yanzu ya raba miliyoyin jama’a da muhallansu, wadda ya haddasa mummunar yanayin zamantakewa mafi tsanani a fadin duniya.

Kiwon Lafiya, Labarai

Post navigation

Previous Post: Na Yi Murabus Ne Don Amurka Ta Keta Haddin Iraniyawa
Next Post: Tinubu Ya Bayyana ‘Yan Bindiga Da Cewa Ruwa Yakarewa Dan Kada

Karin Labarai Masu Alaka

Sarkin Musulmi Ya Ziyarci Shugaba Bola Tinubu Afrika
Usman Maiyama Ne Gwarzon Kamun Kifin Argungu Bana Labarai
Majalisar Dokokin Kamaru Ta Amince Da Wasu Sauye Sauye Afrika
Tsohon Gwamnan Kano, Malam Ibrahim Shekarau Ya Koma Jam’iyyar APC Afrika
Shugaba Tinubu Ya Shiga Takara Wa’adi Na Biyu Afrika
Gwamnan Jihar Zamfara Dauda Lawal Ya Bar PDP Ya Koma APC Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • An Bude Makarantu A Najeriya Najeriya
  • Jami’ai Daga Amurka Sunce Yakin Amurka Da Iran Zaizo Karshe Amurka
  • Tsohuwar Ministan Albarkatun Mai Ta Bayyana A Kotu Najeriya
  • Iran Ta Tsagaita Kai Hare Hare Makwabta Afrika
  • Sarkin Gombe Yayin Hawan Tudun Wada Labarai
  • Najeriya Ta Mika Koke Ga FIFA Tana Zargin DR Congo Ta Sanya ‘Yan Wasan Da Basu Cancantaba Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Sun Hallaka Mutane 30 A Jihar Neja Najeriya
  • Yaki Tsakanin Rasha Da Ukraine Yayi Ajalin ‘Yan Ghana 50 Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.