Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Tsohuwar Ministan Albarkatun Mai Ta Bayyana A Kotu
Published: January 28, 2026 at 10:49 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Tsohuwar ministar albarkatun man fetur ta Nigeria Diezeni Allison Madueke ta karbi cin Hanci, ciki har da kayan sawa, da amfani da manyan gidaje mallakin ‘yan kasuwa masu bukatar kwangiloli masu tsoka daga masana’antar man fetur da na iskar gas, a cewar masu gabatar da kara, yayin gurfanar da ita gaban kotu ranar Talata.

Allison Madueke ta rike mukamin ministan albarkatun man fetur na kasa tsakanin shekarar 2010 zuwa 2015, karkashin mulkin Goodluck Jonathan, kuma ta rike mukamin shugaban kasashe masu arzikin man fetur wato OPEC, na kankanin lokaci. Ta kasance mace ta farko da ta rike duk wadannan mukamai.

Allison Madueke me shekaru 65 a duniya ta kasance daya daga cikin fitattun jami’an da suka rike mukami a fannin makamashi da ke fuskantar tuhuma a kotu kan aikata laifin almundahana, bayan an tuhume ta a shekarar 2023 da laifuka biyar na karban cin hanci, da kuma yin makarkashiyar bada cin hanci, abin da ta Musanya.

Mai gabatar da kara Alexandra Healy ta fada a wata kotu da ke birnin Landan, cewa Allison Madueke na zaman daula ne a Landan inda ta ke yawan zama, daga abin da take samu daga mutane masu bukatar kwangila daga kamfanonin Nigeria.

Healy ta ce an bawa Allison Madueke damar zama a gidaje masu alfarma, da kuma amfani da kayan alatu masu tsada, daga mutanen da suka yarda cewa zata yi amfani da mukamin ta don samar musu abin da suke bukata.

Ta kara da cewa, babu wata hujja da ta nuna cewa Allison Madueke ta bada kwangila ga wadanda basu cancanta ba, amma ba daidai bane ta karbi kyaututtuka daga wadanda ke kawsuwanci da kamfanonin gwamnati.

Allison Madueke ta zauna a akwatin tuhuma a kotu tare da wata mai zartarwa a kamfanin man fetur, Olatimbo Ayinde, me shekaru 54, wadda ake tuhuma da laifi daya na acin hanci, da yake alaka da Allison Maduek, da kuma wani laifin da ban na tuhumar bawa jami’in gwamnatin wata kasa cin hanci.

Yaya ga Allison Madueke, Doye Agama, me shekaru 69, shi ma ana tuhumar sa da kulle-kullen bada cin hanci da ke da alaka da cocin sa, kuma yana sauraron karar ne da hanyar video saboda dalilin rashin lafiya.

Ayinde da Agama ma sun musanta zargin da ake yi a kan su.

Ana zargin Allison Madueke da Karbar kayayyakin kudade daga mutane da ke da alaka da masana’antun man fetur na Nigeria, da suka hada da amfani da mota da direba da jirgin saman yawo.

An kuma zarge ta da sa wani dan kasuwa a Nigeria, Benedict Peters da biyawa dan ta kudin makaranta, wanda akwai sunan sa a tuhumar, amm ba zai fuskanci shari’a ba.

Najeriya

Post navigation

Previous Post: An Tsinci Gawar Yarinya A Gombe
Next Post: Hukumar IMF Tana Naziri Domin Kara Bada Lamuni Ga Kasar Zambiya

Karin Labarai Masu Alaka

Suvr Jahun: Ya Kamata Obasanjo Ya Bar Al’umar Ƙasa Su Fito Da Wadda Suke So 2027 Najeriya
Sojojin Najeriya Sun Kwato Mutane Daga Hannun Masu Garkuwa Najeriya
Gwamnan Jihar Adamawa Fintiri Ya Koma APC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Akwai Alamar Shawarwari Tsakanin Amurka Da Turai Zai Kawo Karshen Yakin Rasha Amurka
Gobara Ta Lalata Shaguna Da Gidajen Abinci A Gombe Labarai
Majalisar Dottawa Ta Kafa Komitin Dokar Zabe Najeriya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Kungiyar Mata Manoma A Najeriya Ta Raba Kyautar Abinci A Gombe
  • Ambaliyar Ruwa Yayi Ajalin Mutane A Nairobi
  • ‘Yan Sandan Najeriya Sunyi Nasarar Hallaka ‘Yan Ta’adda A Katsina
  • Iran Ta Tsagaita Kai Hare Hare Makwabta
  • Shugaban Amurka Ya Ya Bukaci Iran Ta Mika Wuya

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • INEC Mayar Da Lokacin Zaɓen 2027 Kafin Azumi Najeriya
  • Kotun Tarayya Ta Yankewa Nnamdi Kanu Daurin Rai-da-Rai Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Iran Ta Rufe Sararin Samaniyar Ta Labarai
  • Nnamdi Kanu Ya Nemi A Mayar Da Shi Abuja Daga Gidan Yarin Sokoto Labarai
  • Take Hakkin Dan Adam Zai Haifar Da Juyin Juya Hali A Najeriya Najeriya
  • An Kubutar Da Wani Wanda Mahaifinsa Ya daure Da Sarka Tsawon Shekaru 17 A Bauchi Labarai
  • Afirka Ta Kudu Ta Samu Rigakafin Cutar Boro Afrika
  • Kungiyar Enyimba: Bamu Da Niyyar Rage Albashin ‘Yan-Wasa Wasanni
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.