Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Amurka Da Isra’ila Sunkai Hari Kan Iran
Published: March 1, 2026 at 5:01 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Amurka da Isra’ila sun kai hari kan Iran yau Asabar, inda suka auna manyan shugabannnin kasar, suna masu kiran da a kifar da gwamnatin kasar, ita kuma Iran ta maida martani tare da harba makamai masu linzami kan Isra’ila da kasashe makwabta.

Shugaba Donald Trump, a mataki da ake kallo a zaman kasada mafi girma a manufofin harkokin wajen gwamnatinsa, ya kaddamarda yaki kan kasar da Amurka take kallo a zaman makiyarta na shekaru masu yawan gaske, yace harin ta kai shine da nufin kawar da barazana, da kuma tabbatar da ganin Iran bata habaka makaman Nukiliya ba.

Yayi kira ga jami’an tsaron kasar su ajiye makaman su, daga nan ya gayyaci al’umar kasar su kifar da gwamnatin kasar da zarar an kawo karshen hare hare da ake kaiwa kan kasar.

Tehran ta kira harin da aka fara da safiyar ranar asabar kuma ya auna sassa daban daban na kasar, da cewa hari da aka kai mata ba tare da takala ba, kuma baya bisa doka.

Tashar talabijin ta kasar da ake kira -Al-Alam, tace shugaban addinin kasar Ali Khameni, wadda ba’a ji daga gareshi ba zuwa yanzu, zai yi jawabi nan ba da jumawa ba.

A birane a duk fadin kasar, karar fashe fashe sun janyo tsoro. Mazauna biranen suna gaggawar kwaso yara daga Makaranta, da gudu daga wurare da suke zaton za’a kai wa hari.

Isra’ila ta hana jama’a yin tarurruka, ta rufe makarantu da masana’antu, kuma ta kawashe maras lafiya a asibitoci zuwa wurare dake karkashin kasa, a dai dai lokacin da Iran ta harba makamai masu linzami da ta auna kan Isra’ila, a zaman martanin harin da Amurka da Isra’ila suka kai mata.

Ministan tsaron Isra’ila, Israel Katz, ya ayyana dokar ta baci a duk fadin kasar, ya gargadi jama’a dangane da hare hare da Iran zata kai mata da makamai masu linzami da jirage da basu da matuka.

Amurka, Labarai, Sauran Duniya

Post navigation

Previous Post: Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran
Next Post: Babban Sakataren MDD Yayi Allah Wadai Da Matakin Soja A Gabas Ta Tsakiya

Karin Labarai Masu Alaka

Wasu Muhimman Abubuwa Da Najeriya Ba Zata Manta Da Su Ba A 2025 Labarai
Jami’an Diflomasiyyar Iran Dana Amurka Sun Tattauna A Kasar Oman Afrika
Bankin Duniya Zaibawa Kasar Mozambique Lamunin Dala Bilyan Shida Labarai
Amurka Ta Kai ‘Yan Cirani Kamaru Afrika
Shugaban Amurka Zai Sake Aika Jirgin Yaki Gabas Ta Tsakiya Amurka
NDLEA Ta Fara Binciken Kwakwaf Akan Wasu ‘Yan Mata Dake Kai Kwaya Gidan Yari Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Harin Iran A Kasar Saudiya Ya Haifar Da Tattaunawa Tsakanin Shugabanni
  • An Kaiwa Sojojin Ghana Hari Da Makami Mai Linzami
  • Kasar Ghana Zata Sauya Inda Take Kai Sarrafa Gwal
  • ‘Yan Bindiga Sun Hallaka Sojoji 15 Da Wasu Fararen Hula A Benin
  • Hukumomi A Kasar Syri Lanka Suna Kokarin Fidda Jirgin Yakin Iran Daga Kasar

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Aikin Layin Dogon Kasar Uganda Zai Hade Kasar Da Tanzania Da Kwango Kimiya
  • Yaki Ta Sararin Samaniya Ya Cigaba Tsakanin Amurka, Isra’ila Da Iran Afrika
  • Gwamnatin Jihar Kano Zata Kashe Makudan Kudade Ga Jama’ar Kano! Najeriya
  • Kotu A Birnin Tarayya Abuja Ta Bada Belin Tsohon Minista Abubakar Malami Najeriya
  • Gobara Ta Tashi A Makarantar Koyon Jinyar Dabbobi Dake Jihar Kano Najeriya
  • Hadakar Gwamnatin Najeriya Da Amurka Ne Suka Kai Hari Sokoto Najeriya
  • Sabon Jadawalin Gasar Kwalon Kafa Ta Turai 2026 Wasanni
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.