Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • APC: Tinubu Da Shettima Za Su Sake Neman Wa’adi Na Biyu A 2027 Afrika
  • Sabuwar Sakatariyar Ƙungiyar Gwamnonin Arewa Za Ta Ƙarfafa Ayyukan Ci Gaban Yankin Afrika
  • TIC Dutse Ta Nemi Ƙarin Tallafin Gwamnatin Jigawa Don Faɗaɗa Ayyukanta Afrika
  • Gobara Ta Lalata Babban Zauren Majami’ar ECWA Gospel A Gombe Afrika
  • Gombe: ‘Yan Sanda Sun Tarwatsa Ƙungiyar Masu Fashi Da Damfara Ta Yanar Gizo Afrika

Amurka Da Isra’ila Sunkai Hari Kan Iran
Published: March 1, 2026 at 5:01 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Amurka da Isra’ila sun kai hari kan Iran yau Asabar, inda suka auna manyan shugabannnin kasar, suna masu kiran da a kifar da gwamnatin kasar, ita kuma Iran ta maida martani tare da harba makamai masu linzami kan Isra’ila da kasashe makwabta.

Shugaba Donald Trump, a mataki da ake kallo a zaman kasada mafi girma a manufofin harkokin wajen gwamnatinsa, ya kaddamarda yaki kan kasar da Amurka take kallo a zaman makiyarta na shekaru masu yawan gaske, yace harin ta kai shine da nufin kawar da barazana, da kuma tabbatar da ganin Iran bata habaka makaman Nukiliya ba.

Yayi kira ga jami’an tsaron kasar su ajiye makaman su, daga nan ya gayyaci al’umar kasar su kifar da gwamnatin kasar da zarar an kawo karshen hare hare da ake kaiwa kan kasar.

Tehran ta kira harin da aka fara da safiyar ranar asabar kuma ya auna sassa daban daban na kasar, da cewa hari da aka kai mata ba tare da takala ba, kuma baya bisa doka.

Tashar talabijin ta kasar da ake kira -Al-Alam, tace shugaban addinin kasar Ali Khameni, wadda ba’a ji daga gareshi ba zuwa yanzu, zai yi jawabi nan ba da jumawa ba.

A birane a duk fadin kasar, karar fashe fashe sun janyo tsoro. Mazauna biranen suna gaggawar kwaso yara daga Makaranta, da gudu daga wurare da suke zaton za’a kai wa hari.

Isra’ila ta hana jama’a yin tarurruka, ta rufe makarantu da masana’antu, kuma ta kawashe maras lafiya a asibitoci zuwa wurare dake karkashin kasa, a dai dai lokacin da Iran ta harba makamai masu linzami da ta auna kan Isra’ila, a zaman martanin harin da Amurka da Isra’ila suka kai mata.

Ministan tsaron Isra’ila, Israel Katz, ya ayyana dokar ta baci a duk fadin kasar, ya gargadi jama’a dangane da hare hare da Iran zata kai mata da makamai masu linzami da jirage da basu da matuka.

Amurka, Labarai, Sauran Duniya

Post navigation

Previous Post: Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran
Next Post: Babban Sakataren MDD Yayi Allah Wadai Da Matakin Soja A Gabas Ta Tsakiya

Karin Labarai Masu Alaka

Amurkawa Sun Nuna Bacin Rai Saboda Yawaita Kashe ‘Yan Kasar Amurka
Atiku Ya Zargi Gwamnati Da Kama ‘Yan Adawa Labarai
Sanata Goje: Sakamakon Zaben Daga Abuja Zai Fito Afrika
Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
China Da Jamhuriyar Dimokraɗiyya Kwango Sun Kulla Yarjejeniya Afrika
Tinubu: Mun Ware Biliyan 42 Don Inganta Lafiyar ‘Yan-Kasa Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • APC: Tinubu Da Shettima Za Su Sake Neman Wa’adi Na Biyu A 2027
  • Sabuwar Sakatariyar Ƙungiyar Gwamnonin Arewa Za Ta Ƙarfafa Ayyukan Ci Gaban Yankin
  • TIC Dutse Ta Nemi Ƙarin Tallafin Gwamnatin Jigawa Don Faɗaɗa Ayyukanta
  • Gobara Ta Lalata Babban Zauren Majami’ar ECWA Gospel A Gombe
  • Gombe: ‘Yan Sanda Sun Tarwatsa Ƙungiyar Masu Fashi Da Damfara Ta Yanar Gizo

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Duk Da Rauni Daya Samu Sakamakon Hari Mojtaba Khameni Yafara Aiki Labarai
  • ‘Yan Gudun Hijira A Kasar Libya Suna Fuskantar Cin Zarafi Afrika
  • Rundunar ‘Yan Sanda Sun Ceto Wani Daga Hannun Masu Garkuwa Najeriya
  • Gwamna Zulum: Ya Bukaci Sojoji Su Cigaba Da Yakar Boko Haram Da ISWAP Labarai
  • ‘Yan Jarida Sunyi Mummunan Hatsari A Bauchi Labarai
  • Tsohon Ma’aikacin VOA Saleh Shehu Ashaka Ya Rasu Afrika
  • Gwamnatin Gombe Ta Kaddamar Da Sabon Ofishin GOGIS Don Inganta Tsarin Filaye Afrika
  • ‘Yan Agajin Izalar Jos Sunyi Hatsari Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.