Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19 Afrika
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027 Afrika
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki Afrika
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko Afrika

Amurka Da Isra’ila Sunkai Hari Kan Iran
Published: March 1, 2026 at 5:01 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Amurka da Isra’ila sun kai hari kan Iran yau Asabar, inda suka auna manyan shugabannnin kasar, suna masu kiran da a kifar da gwamnatin kasar, ita kuma Iran ta maida martani tare da harba makamai masu linzami kan Isra’ila da kasashe makwabta.

Shugaba Donald Trump, a mataki da ake kallo a zaman kasada mafi girma a manufofin harkokin wajen gwamnatinsa, ya kaddamarda yaki kan kasar da Amurka take kallo a zaman makiyarta na shekaru masu yawan gaske, yace harin ta kai shine da nufin kawar da barazana, da kuma tabbatar da ganin Iran bata habaka makaman Nukiliya ba.

Yayi kira ga jami’an tsaron kasar su ajiye makaman su, daga nan ya gayyaci al’umar kasar su kifar da gwamnatin kasar da zarar an kawo karshen hare hare da ake kaiwa kan kasar.

Tehran ta kira harin da aka fara da safiyar ranar asabar kuma ya auna sassa daban daban na kasar, da cewa hari da aka kai mata ba tare da takala ba, kuma baya bisa doka.

Tashar talabijin ta kasar da ake kira -Al-Alam, tace shugaban addinin kasar Ali Khameni, wadda ba’a ji daga gareshi ba zuwa yanzu, zai yi jawabi nan ba da jumawa ba.

A birane a duk fadin kasar, karar fashe fashe sun janyo tsoro. Mazauna biranen suna gaggawar kwaso yara daga Makaranta, da gudu daga wurare da suke zaton za’a kai wa hari.

Isra’ila ta hana jama’a yin tarurruka, ta rufe makarantu da masana’antu, kuma ta kawashe maras lafiya a asibitoci zuwa wurare dake karkashin kasa, a dai dai lokacin da Iran ta harba makamai masu linzami da ta auna kan Isra’ila, a zaman martanin harin da Amurka da Isra’ila suka kai mata.

Ministan tsaron Isra’ila, Israel Katz, ya ayyana dokar ta baci a duk fadin kasar, ya gargadi jama’a dangane da hare hare da Iran zata kai mata da makamai masu linzami da jirage da basu da matuka.

Amurka, Labarai, Sauran Duniya

Post navigation

Previous Post: Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran
Next Post: Babban Sakataren MDD Yayi Allah Wadai Da Matakin Soja A Gabas Ta Tsakiya

Karin Labarai Masu Alaka

Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Gana Da Shugaban Makaman Nukiliya Afrika
An Kusa Kawo Karshen Matsalolin Tsaro A Jihar Filato Afrika
Zulum Ya Tallafa Wa Mambobin NYSC Da Naira Miliyan 8.2 A Borno Afrika
Meyasa Israela Take Hana Kaiwa Gaza Kayan Tallafi Afrika
‘Yan Jarida Sunyi Mummunan Hatsari A Bauchi Labarai
NUJ Gombe Ta Ƙarfafa Bin Ɗa’a A Aikin Jarida, Ta Kaddamar Da Kwamitin Ladabtarwa Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Lewandowski: Zan Kokarta Zura Kwallo Ta 90 Don Kafa Tarihi A Poland Wasanni
  • Akwai Bukatar APC Tayi Gyare-Gyare Kafun Zabe Afrika
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari Afrika
  • Zaman Lafiya Yafara Dawowa A Sudan Afrika
  • Kasar Spain Zata Bada Diyya Ga Iyalen Wadanda Da Suka Rasu A Hatsarin Jirgin Kasa Labarai
  • Tattalin Arzikin Najeriya Ya Farfardo Bisa Samun Wasu Sauye Sauye Labarai
  • PDP Ta Tsayar da Goodluck Jonathan Takarar Shugaban Kasa Afrika
  • Menene Illar Yada Labaran Karya A Kafofin Sada Zumunta Na Zamani Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.