Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro Labarai
  • Za A Cigaba Da Tattaunawa Domin Kawo Karshen Yakin Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Sanatan Nasarawa Ta Arewa Ya Rasu A Kasar India
Published: January 2, 2026 at 12:54 PM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: January 2, 2026

Sanata Godiya Akwashiki, mai wakiltar Nasarawa ta Arewa, ya rasu yana da shekaru 52 a wani asibiti da ke ƙasar Indiya.

Rahotanni sun ce ya dade yana fama da rashin lafiya, kuma yana karɓar magani a Indiya kafin rasuwarsa.

Marigayi Akwashiki, wanda aka haife shi a ranar 3 ga Agusta, 1973, a Angba Iggah da ke ƙaramar hukumar Nasarawa Eggon, ya taɓa rike mukamin shugaban masu rinjaye da mataimakin kakakin majalisar dokokin jihar Nasarawa, kafin daga bisani ya zama Sanata a shekarar 2019 karkashin jam’iyyar APC kuma an sake zaɓensa a 2023 karkashin jam’iyyar SDP.

Wani babban mataimaki ga marigayin Sanata, Ajegena Likita Ibrahim, ya tabbatar da rasuwar inda ya bayyana mutuwarsa a matsayin “babban rashi”.

Ibrahim ya shaida wa Daily Trust cewa suna ci gaba da tuntuba da ‘yan uwa a Indiya, amma har yanzu ba a fara shirye-shiryen dawo da gawar Sanata Akwashiki zuwa Najeriya domin jana’iza ba.

Najeriya

Post navigation

Previous Post: Kotu Ta Bada Belin Kwamishinan Kudin Jihar Bauchi
Next Post: Gwamnan Jihar Filato Ya Karbi Katin APC

Karin Labarai Masu Alaka

Ministan Harkokin Wajen Najeriya Yayi Murabus Afrika
Shugabannin Sojojin Najeriya sun Kai Ziyarar Aiki Maiduguri  Afrika
Gwamnatin Gombe Ta Kulla Yarjejeniyar Da New Zealand Kimiya
Jami’an tsaro sama da dubu biyar ne zasuyi aikin tabbatar da tsaro Alokacin bikin karamar sallah a Jihar Nejan Najeriya. Najeriya
Gwamna Inuwa Yahaya ya Rusa Majalisar Zantaswa ta Jihar Gombe Labarai
Majalisar Tattalin Arzikin Najeriya Ta Bawa Gwamnan Kebbi Mukamin Kyautata Harkar Kiwo Najeriya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jami’an Askarawa A Zamfara Sun Kama Na’urorin Fashewa Da Makudan Kuɗaɗe
  • Jami’yar ADC A Najeriya Ta Kori Nafiu Bala
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro
  • ‘Yan Sanda Sun Kama Mutane 33 Bisa Zargin Kai Hari A Jihar Kwara
  • Papa Roma Leo Yayi Gargadi Game Da Rushewar Dimokraɗiyya

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Farmakin Da Aka Kai Makarantar Mata A Iran Yayi Ajalin Yara Da Dama Afrika
  • Masu Goyon Bayan Palasdinawa Sunyi Gangamin Zanga Zanga A Australia Labarai
  • Babangida: Hakika Abiola Ya Lashe Zaben Watan Yuni 1993 Labarai
  • Sojojin Najeriya Sun Kwato Mutane Daga Hannun Masu Garkuwa Najeriya
  • Kasar Ukraine Tayi Watsi Da Shiga Kungiyar NATO Labarai
  • Anakan Bincike Wajen Gano Dan Bindigar Da Ya Kashe Dalibai Biyu A Jihar Rhode Island Amurka
  • Tsananin Sanyi Ya Kashe Mutane 38 A Amurka Amurka
  • Matatar Man Dangote Ta Kara Yawan Mai Dake Zuwa Kasashen Afirka Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.