Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

Boko Haram Sun Farmaki Sansanin Sojoji A Borno
Published: January 22, 2026 at 8:06 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Wasu majiyoyin tsaro a Najeriya sun ce an kashe sojoji akalla 8, aka raunata wasu 50 a lokacin da ‘yan ta’addan kungiyar Boko Haram suka kai farmaki a kan wani sansanin sojoji dake jihar Borno.

Majiyoyin suka ce ‘yan bindigar na Boko Haram sun isa a kan babura da motoci masu sulke a ranar litinin.

Wata majiyar soja a Najeriya ta fadawa kamfanin dillancin labarai na Reuters cewa wannan sansani an kafa shi ne a wani bangare na farmakin da ake kaiwa da nufin tumbuke ‘yan Boko Haram daga wani yankin da suka lakaba ma suna Timbuktu, wanda yanki ne da ya tashi daga Damboa zuwa Maiduguri, ya yi yamma zuwa Ngamdu, ya sake yin gabas zuwa Damboa.

A wata sanarwar da ta bayar ranar laraba, rundunar sojojin Najeriya ta ce sojoji sun kori ‘yan Boko Haram daga sansanoninsu da dama dake cikin wannan yanki na Timbuktu, suka kuma wargaza shirye-shiryen kai hare-hare da motocin da aka dana bama-bamai cikinsu.

Rundunar ta ce dakaru sun samu nasarar katse hanzarin wata motar da aka shake ta bama-bamai, amma wata a bayanta ta samu halin shigewa cikin inda sojojin suka yi daga ta kashe wasu sojoji da fararen hula masu aikin sa kai, wadanda aka fi sani da suna Civilian-JTF.

Wani dan rundunar Civilian-JTF ya tabbatar da wannan fada da aka gwabza yana mai fadin cewa ‘yan Boko Haram da suka kai harin sun ninka sojojin dake sansanin.

Tuni dai rundunar sojojin ta janye wadannan sojoji zuwa babban sansaninta dake garin Damboa kuma an kwashi gawarwakin wadanda suka mutu da wadanda suka ji rauni zuwa asibitin sojojin dake barikin Maimalari a garin Maiduguri.

Tsaro

Post navigation

Previous Post: Tarayyar Turai Zasu Kirkiro Sojojin Haɗin Gwiwa
Next Post: Gwamnatin Tarayya: Bikin Al’adun Argungu Ya Karbu A Idon Duniya

Karin Labarai Masu Alaka

Mayakan RSF A Sudan Suna Sace Kananan Yara A Lokacin Yake-Yaken Kasar Afrika
Gwamnonin Arewa Sunyi Allah Wadai Da Harin Jos Afrika
‘Yan Sandan Gombe Sun Fara Kama Motocin Da Ba Su Da Lambar Rajista ko Masu Boye Lambobinsu Afrika
‘Yan Bindiga Sun Jikkata Mutane A Arewacin Kasar Benin Afrika
Mamakon Ruwan Sama Da Iska Ya Hallaka Mutane Uku A Jihar Yobe Labarai
Zargin Fitar Da Bayanan Masu Zabe A Najeriya Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk. Wasanni
  • Kotun Daukaka Kara A Faransa Zata Tabbatar Da Hukuncin ‘Yan Jam’iyyar Ra’ayin Rikau Labarai
  • Amurka Ta Kwace Jirgin Mai Mallakar Rasha Amurka
  • Nasarawa Ce Zakara A Wasan Kwallon Kafa Ta Kurame 2025 Wasanni
  • Masana: ‘Yancin Kasashen Afrika A Rubuce Yake Ba A Zahirance Ba Najeriya
  • Wata Tankar Mai Ta Kife A Apapa Legas Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Anyi Bikin Cikar Tsohon Shugaban Kasa Abdulsalami Shekaru 84 Afrika
  • Bayan Shafe Shekaru Hudu A Mulki Sarkin Hausawan Ibadan Ya Rasu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.