Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Boko Haram Sun Farmaki Sansanin Sojoji A Borno
Published: January 22, 2026 at 8:06 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Wasu majiyoyin tsaro a Najeriya sun ce an kashe sojoji akalla 8, aka raunata wasu 50 a lokacin da ‘yan ta’addan kungiyar Boko Haram suka kai farmaki a kan wani sansanin sojoji dake jihar Borno.

Majiyoyin suka ce ‘yan bindigar na Boko Haram sun isa a kan babura da motoci masu sulke a ranar litinin.

Wata majiyar soja a Najeriya ta fadawa kamfanin dillancin labarai na Reuters cewa wannan sansani an kafa shi ne a wani bangare na farmakin da ake kaiwa da nufin tumbuke ‘yan Boko Haram daga wani yankin da suka lakaba ma suna Timbuktu, wanda yanki ne da ya tashi daga Damboa zuwa Maiduguri, ya yi yamma zuwa Ngamdu, ya sake yin gabas zuwa Damboa.

A wata sanarwar da ta bayar ranar laraba, rundunar sojojin Najeriya ta ce sojoji sun kori ‘yan Boko Haram daga sansanoninsu da dama dake cikin wannan yanki na Timbuktu, suka kuma wargaza shirye-shiryen kai hare-hare da motocin da aka dana bama-bamai cikinsu.

Rundunar ta ce dakaru sun samu nasarar katse hanzarin wata motar da aka shake ta bama-bamai, amma wata a bayanta ta samu halin shigewa cikin inda sojojin suka yi daga ta kashe wasu sojoji da fararen hula masu aikin sa kai, wadanda aka fi sani da suna Civilian-JTF.

Wani dan rundunar Civilian-JTF ya tabbatar da wannan fada da aka gwabza yana mai fadin cewa ‘yan Boko Haram da suka kai harin sun ninka sojojin dake sansanin.

Tuni dai rundunar sojojin ta janye wadannan sojoji zuwa babban sansaninta dake garin Damboa kuma an kwashi gawarwakin wadanda suka mutu da wadanda suka ji rauni zuwa asibitin sojojin dake barikin Maimalari a garin Maiduguri.

Tsaro

Post navigation

Previous Post: Tarayyar Turai Zasu Kirkiro Sojojin Haɗin Gwiwa
Next Post: Gwamnatin Tarayya: Bikin Al’adun Argungu Ya Karbu A Idon Duniya

Karin Labarai Masu Alaka

Gwamnatin Kano Zata Dauki Mataki Game Da Kisan Dorayi Tsaro
Shugaban Amurka Ya Ya Bukaci Iran Ta Mika Wuya Afrika
Tinubu: Zamu Kara Kyautata Samar Da Kayan Aiki Ga Jami’an Tsaro Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Ranar Talata Amurka Da Isra’ila Sun Cigaban Da Kai Farmaki Iran Afrika
Shugaban Kasar Tunisiya Ya Tsawaita Dokar Da Baci A Kasar Labarai
Kungiyar Kwadago Ta NLC Ta Gudanar Da Zanga-Zanga Bisa Matsalar Tsaro Tsaro

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Kungiyar Gwamnonin Arewacin Najeriya Tayi Kakkausar Lafazi Game Da Harin Maiduguri
  • Tinubu, Akpabio da Ministoci 9 Zasu Tafi Ƙasar Birtaniya
  • Tinubu Ya Aika Manyan Hafsoshin Tsaro Borno
  • Lauyoyi Sun Gurfanar Da Wani A Kotu Bisa Fasa Korin Kiyashi A Kenya
  • Anfara Gangamin Kafa Dokoki Masu Tsanani Ga ‘Yan Luwadi A Senegal

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • ‘Yan Bindiga Sun Hallaka Mutane A Kauyuka Dake Yammacin A Najeriya Najeriya
  • Eziekel Gomos Ya Zamo Babban Daraktan Sakatariyar Zauren Gwamnonin Arewa Najeriya
  • Amurka Ta Kama Wani Jirgin Dakon Mai Amurka
  • Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Afrika
  • Bola Ahmed Tinubu Ya Soke Bashin Da Gwamnati Take Bin NNPC Najeriya
  • Shirin Manuniya Kashi Na Daya, Yau Juma’a 11.21.25 Shirye-Shirye
  • Tattalin Arzikin Kasar Botswana Zai Farfado Afrika
  • Akwai Bukatar Bin Dokokin Tuki A Kan Hanyoyi Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.