Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe Afrika
  • Hukumomin Bada Agaji Sun Fadakar Da Al’ummar Jihar Gombe Afrika
  • Ana Cigaba Da Shirye-Shiryen Fara Gasar Kwallon Sarakuna A Gombe Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Zata Samar Da Sabbin Dakunan Karatun Dalibai Afrika
  • Gwamnatin Tarayya Ta Cire Sharadin Rubuta UTME Ga Masu Neman Shiga Kwalejojin Ilimi Afrika

Shugaba Tinubu Ya Bukaci Samar Da Zaman Lafiya A Filato
Published: April 29, 2026 at 3:29 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

A wani mataki na fitar da jihar Filato dake Najeriya daga kangin tashe-tashen hankula da suka ƙi ci suka ƙi cinyewa, Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya gana da shugabannin jihar, inda ya ba su umarnin komawa gida su fuskanci juna da zuciya ɗaya domin samar da dawwamamen zaman lafiya.

Haka zalika, Gwamnatin Tarayya ta amince da sakin kudi har Naira Biliyan biyu (N2bn) a matsayin tallafin gaggawa ga mutanen da harin ranar 29 ga watan Maris ya rutsa da su a unguwar Anguwan Rukuba da ke Karamar Hukumar Jos ta Arewa.

Yayin taron wanda aka kwashe sa’o’i uku ana tattaunawa a fadar Shugaban Kasa da ke Abuja ranar Talata, Shugaba Tinubu ya bayyana cewa lokaci ya yi da shugabanni a kowane mataki za su cire son zuciya, su rungumi juna domin kawo karshen asarar rayuka da dukiyoyi.

“Ba maganar biki muke yi a nan ba,” in ji Shugaban Kasan. “Muna nan ne domin mu faɗawa juna gaskiya. Idan ana amfani da matasa ana rura wutar gaba da kisan juna, ku shugabanni ya kamata ku fara bincikar kanku.”

Shugaban ya kuma kalubalanci tawagar, karkashin jagorancin Gwamna Caleb Mutfwang, da su koma su duba duk wasu rahotannin tsofaffin kwamitoci (White Papers) da aka taɓa yi kan rikicin jihar, su fito da hanyoyin da za a bi wajen aiwatar da su.

Tawagar mai mutum 32 ta haɗa da tsofaffin gwamnonin jihar; Sanata Simon Lalong, Sanata Jonah Jang, Joshua Dariye da Sir Fidelis Tapgun. Sauran sun hada da Sarkin Wase, Mai Martaba Mohammed Haruna; Gbong Gwon Jos, Da Jacob Gyang Buba; Shugaban kungiyar CAN na jihar, da kuma wakilan matasan Musulmi da Kirista.

A nashi ɓangaren, Gwamna Mutfwang ya nuna farin cikinsa, inda ya bayyana cewa wannan ne karon farko da dukkan tsofaffin gwamnonin jihar suka zauna a daki guda domin tattauna makomar jihar. Ya bayyana cewa wannan wata sabuwar baraka ce ta hadin kai da za ta taimaka wajen maido da martabar “Gidan Zaman Lafiya da Shakatawa.”

Shima Mai Martaba Gbong Gwon Jos, Da Jacob Gyang Buba, ya jinjinawa Shugaban Kasan, ya kuma bukaci a tura karin jami’an tsaro da kuma sanya na’urorin CCTV a lungu da sako na birnin Jos. Haka zalika, ya roki Shugaban da ya taimaka wajen ganin ’yan gudun hijira (IDPs) sun koma gidajen iyaye da kakanninsu kafin damuna ta kankama.

Taron ya zo ne a matsayin cika alkawarin da Shugaba Tinubu ya yi na zama da masu ruwa da tsaki na jihar bayan munanan kashe-kashen da aka yi a watan Maris, inda ya jaddada cewa ba za a zuba ido ana kisan mutane ba tare da an hukunta wadanda ke rura wutar rikicin ba.

Masana na ganin cewa wannan zama na Abuja zai iya zama silar kawo karshen shekaru da dama na gaba da jidali a jihar, muddin shugabannin suka yi amfani da wannan damar wajen girmama juna da adalci.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Za’ayi Auren Zawarawa Dubu Uku A Kano
Next Post: Mohammed Abdullahi Abubakar Ya Sayi fom Don Tsayawa Takarar kujeran Gwamnan Bauchi A APC 2027

Karin Labarai Masu Alaka

Sojin Saman Najeriya Sunyi Gagarumar Nasara A Yankin Borno Najeriya
Gwamnatin Gombe Ta Kulla Yarjejeniyar Da New Zealand Kimiya
Jihar Gombe Ta Saka Hannu Kan Yarjejeniya Da Kamfanonin Tunisiya Kimiya
Jagoran Addinin Kirista A Kaduna Ya Rabawa Fiye Da Musulmai Dubu Kayan Abincin Azumi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Gwamnatin Kasar Ghana Ta Rage Farashin Cocoa Afrika
An Garkame Wani Babban Soja A Kasar Australiya Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe
  • Hukumomin Bada Agaji Sun Fadakar Da Al’ummar Jihar Gombe
  • Ana Cigaba Da Shirye-Shiryen Fara Gasar Kwallon Sarakuna A Gombe
  • Gwamnatin Najeriya Zata Samar Da Sabbin Dakunan Karatun Dalibai
  • Gwamnatin Tarayya Ta Cire Sharadin Rubuta UTME Ga Masu Neman Shiga Kwalejojin Ilimi

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Jami’an Askarawa A Zamfara Sun Kama Na’urorin Fashewa Da Makudan Kuɗaɗe Afrika
  • An Gudanar Da Addu’oi Ga Mutane 16 Da ‘Yan Bindiga Suka Kashe a Australiya Tsaro
  • Majalisar Dottawa Ta Kafa Komitin Dokar Zabe Najeriya
  • An Gudanar Da Taron Matasan Kasashe 6, Don Kawo Karshen Ta’addanci Wasanni
  • Farashin Danyen Mai Ya Farfado Fiye Da Kashi Daya Sauran Duniya
  • Cutar Zazzabin Lassa Tayi Ajalin Mutum 1 Yayinda Mutane 11 Suka Kamu A Jihar Gombe Najeriya
  • Kadan Daga Cikin Abubuwan Da Suka Faru A 2025 A Nan Amurka Amurka
  • Anyi Jana’izar Mahaifiyar Nasiru El Rufai A Abuja Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.