Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama Afrika
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara Afrika
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe Afrika
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro Afrika
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa Afrika

Kauran Gwandu Zai Inganta Wutan Lantarki A Kebbi
Published: January 5, 2026 at 11:25 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Gwamnan jihar Kebbi, Dr. Nasir Idris (Kauran Gwandu), ya amince da fitar da naira miliyan 650 domin sayewa da girke na’urar wutar lantarki mai karfin 15MVA, da nufin inganta samar da lantarki a fadin jihar.

Sakataren Gwamnatin jihar, Alhaji Yakubu Bala Tafida, ne ya bayyana hakan a ranar Juma’a yayin ganawa da manema labarai a Birnin Kebbi.

A cewar sa, wannan mataki ya nuna jajircewar gwamnatin jihar wajen rage wahalhalun da al’umma ke fuskanta sakamakon rashin tabbataccen wutar lantarki.

Ya kara da cewa duk da cewa rarraba wutar lantarki hakki ne na Kamfanin KAEDCO, gwamnatin jihar ta ga dacewar shiga tsakani domin kare muradun jama’a.

Alhaji Tafida ya kuma bayyana cewa baya ga wannan kudin, gwamnatin Kebbi tana bada tallafin naira miliyan 150 duk wata ga KAEDCO, domin inganta ayyuka da tabbatar da dorewar wutar lantarki a jihar.

Ya yi kira ga al’umma da su ba da hadin kai ta hanyar biyan kudin wutar lantarki akan lokaci, yana mai jaddada cewa hakan zai taimaka matuka wajen dorewar ingantaccen wuta a jihar.

Siyasa

Post navigation

Previous Post: Salmanu: Ci Gaban Wikki Tourist FC Shine A Gaba Na
Next Post: Manchester United Ta Sallami Ruben Amorim

Karin Labarai Masu Alaka

‘Yan Daba Sunkai Hari Kasuwar Waya A Kano Afrika
Kwankwaso Yayi Kakkausar Lafazi Bayan Ficewar Abba Kabir Yusuf Daga NNPP Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Gwamna Inuwa Yahaya Ya Rantsar Da Sabon Shugaban Ma’aikatan Jiha da Kwamishinoni 23 Afrika
Al’ummar Jihar Nasarawa Suna Cecekuce Bisa Tsaida Aliyu Wadada Takarar Gwamna Afrika
An Bukaci Sabbin Shugabanni Su Yi Jagoranci Nagari da Inganta Ayyukan Jama’a Labarai
Shugaba Tinubu Zai Kara Karbo Bashin Dala Miliyan 516 Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Amurka Tace Zata Gama Yakin Iran Cikin Makonni Afrika
  • Tinubu Ya Lashe Zaɓen Fidda Gwanin APC Da Kuri’u Miliyan 11 Afrika
  • Tinubu Ya Aika Manyan Hafsoshin Tsaro Borno Afrika
  • Kasar Afirka Ta Kudu Ta Tsare Wasu Amurkawa Amurka
  • Shugabannin Kiristoci Sun Halarci Filin Idi A Kaduna Domin Nuna Haɗin Kai Afrika
  • Hatsarin Mota Yayi Ajalin Mutum 7 A Gombe Najeriya
  • Za’a Jima Ana Fama Da Tsadar Farashin Mai Afrika
  • Jami’an Tsaron Pakistan Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.