Gwamnan jihar Kebbi, Dr. Nasir Idris (Kauran Gwandu), ya amince da fitar da naira miliyan 650 domin sayewa da girke na’urar wutar lantarki mai karfin 15MVA, da nufin inganta samar da lantarki a fadin jihar.
Sakataren Gwamnatin jihar, Alhaji Yakubu Bala Tafida, ne ya bayyana hakan a ranar Juma’a yayin ganawa da manema labarai a Birnin Kebbi.
A cewar sa, wannan mataki ya nuna jajircewar gwamnatin jihar wajen rage wahalhalun da al’umma ke fuskanta sakamakon rashin tabbataccen wutar lantarki.
Ya kara da cewa duk da cewa rarraba wutar lantarki hakki ne na Kamfanin KAEDCO, gwamnatin jihar ta ga dacewar shiga tsakani domin kare muradun jama’a.
Alhaji Tafida ya kuma bayyana cewa baya ga wannan kudin, gwamnatin Kebbi tana bada tallafin naira miliyan 150 duk wata ga KAEDCO, domin inganta ayyuka da tabbatar da dorewar wutar lantarki a jihar.
Ya yi kira ga al’umma da su ba da hadin kai ta hanyar biyan kudin wutar lantarki akan lokaci, yana mai jaddada cewa hakan zai taimaka matuka wajen dorewar ingantaccen wuta a jihar.


