Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro Labarai
  • Za A Cigaba Da Tattaunawa Domin Kawo Karshen Yakin Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Kauran Gwandu Zai Inganta Wutan Lantarki A Kebbi
Published: January 5, 2026 at 11:25 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Gwamnan jihar Kebbi, Dr. Nasir Idris (Kauran Gwandu), ya amince da fitar da naira miliyan 650 domin sayewa da girke na’urar wutar lantarki mai karfin 15MVA, da nufin inganta samar da lantarki a fadin jihar.

Sakataren Gwamnatin jihar, Alhaji Yakubu Bala Tafida, ne ya bayyana hakan a ranar Juma’a yayin ganawa da manema labarai a Birnin Kebbi.

A cewar sa, wannan mataki ya nuna jajircewar gwamnatin jihar wajen rage wahalhalun da al’umma ke fuskanta sakamakon rashin tabbataccen wutar lantarki.

Ya kara da cewa duk da cewa rarraba wutar lantarki hakki ne na Kamfanin KAEDCO, gwamnatin jihar ta ga dacewar shiga tsakani domin kare muradun jama’a.

Alhaji Tafida ya kuma bayyana cewa baya ga wannan kudin, gwamnatin Kebbi tana bada tallafin naira miliyan 150 duk wata ga KAEDCO, domin inganta ayyuka da tabbatar da dorewar wutar lantarki a jihar.

Ya yi kira ga al’umma da su ba da hadin kai ta hanyar biyan kudin wutar lantarki akan lokaci, yana mai jaddada cewa hakan zai taimaka matuka wajen dorewar ingantaccen wuta a jihar.

Siyasa

Post navigation

Previous Post: Salmanu: Ci Gaban Wikki Tourist FC Shine A Gaba Na
Next Post: Manchester United Ta Sallami Ruben Amorim

Karin Labarai Masu Alaka

Shugaban Kasar Koriya Ta Arewa Ya Zamo Sakataren Jam’iya Mai Mulki Labarai
Zabebben Shugaban Hungary Yace Zaidawo Da Tsarin Dimokraɗiyya Afrika
Netanyahu Yayi Gaggawar Amincewa Da Kasafin Kudin Kasar Afrika
Prime Ministan Senegal Ya Bayyana Shirin Sauya Sheka Afrika
Sojojin Kasar Uganda Sun Bazama Neman Bobi Wine Sakamakon Rikicin Bayan Zabe Siyasa
China Ta Kori Wakilan Majalisar Dokoki Uku A Kasar Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jami’yar ADC A Najeriya Ta Kori Nafiu Bala
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro
  • ‘Yan Sanda Sun Kama Mutane 33 Bisa Zargin Kai Hari A Jihar Kwara
  • Papa Roma Leo Yayi Gargadi Game Da Rushewar Dimokraɗiyya
  • Jiragen Ruwa Suna Biyayya Ga Dokar Hana Ketare Ruwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Kasar India Ta Sayi Iskar Gas Daga Iran Labarai
  • Sabon Jadawalin Gasar Kwalon Kafa Ta Turai 2026 Wasanni
  • Najeriya, Sojoji Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Sama Da 80, Sun Ceto 34 Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Shugaban Kasar Afirka Ta Tsakiya Ya Roki Rasha Ta Taimakawa Kasar Afrika
  • Shugaba Tinubu Yakarawa Mambobin ASUU Kashi 40 Na Albashi Najeriya
  • Gwamnatin Kano Zata Dauki Mataki Game Da Kisan Dorayi Tsaro
  • Kamfanin Mai Mallakar Saudiya Aramco Zai Sanja Hanyar Fitar Da Danyen Mai Labarai
  • Harin Ukraine Yayi Mummunan Barna A Rasha Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.