Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Najeriya Da Maroko Sun Kulla Yarjejeniya Afrika
  • Pantami Ya Bayyana Dalilin Mayar Da Zaben Sa Abuja Afrika
  • Jam’iyar SDP Tana Gudanar Da Babban Taro A Bauchi Afrika
  • Rundunar Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Shirya Taron Masu Ruwa Da Tsaki A Jihar Filato Afrika
  • Najeriya Da Amurka Sun Karfafa Alakar Tsaro Afrika

Kwankwaso Yayi Kakkausar Lafazi Bayan Ficewar Abba Kabir Yusuf Daga NNPP
Published: January 24, 2026 at 5:34 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar NNPP kuma jagoran Kwankwasiyya, Rabiu Musa Kwankwaso, ya sake jaddada tsayuwar sa kan akidun sa na siyasa, yana mai cewa ba zai sayar da ƙa’idojinsa domin amfanin kansa ba.

Kwankwaso ya bayana hakan ne a daidai lokacin da rahotanni ke cewa Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, tare da wasu shugabannin ƙananan hukumomi, wasu ’yan Majalisar Wakilai da wasu mataimaka, sun fice daga jam’iyyar NNPP.

Da yake jawabi ga magoya baya a gidan sa da ke Kano jim kaɗan bayan murabus ɗin gwamnan a ranar Juma’a, Kwankwaso ya ce gwagwarmayar sa ta siyasa tun farko ta ta’allaka ne kan ’yantar da talakawan Najeriya.

“Ni ba na sayarwa ba ne. Akidun siyasar mu ne ke tsayar da ni a kan hanya. Da ace neman riba ta kaina nake yi, da tuni na bi hanya mai sauƙi, kuma da ba ku same ni a nan ba,” in ji shi.

Ya ƙara da cewa ƙungiyar Kwankwasiyya ta tsaya tsayin daka ne bisa ɗabi’u da manufofi na bai ɗaya, ba wai saboda abin duniya ba.

“Manufa da hangen nesan mu ne ke ƙarfafa ni. Da ace kwaɗayi ne ke motsa ni, da tuni na karɓi kuɗi na gudu, kuma da ba ku zo nan nuna goyon baya ba,” ya ƙara da cewa.

Kwankwaso ya kuma buƙaci magoya bayan sa da su fara shiri da wuri gabanin zaɓukan gama-gari na 2027, yana mai gargaɗi kada a yi sakaci.

“Muna buƙatar mutane irin ku da suka sadaukar kuma suka tsaya kan gaskiya. Kada ku yi kasa a gwiwa, domin wata rana za mu cimma burinmu,” in ji shi.

Da yake magana kan abubuwan da ke faruwa a Kano a baya-bayan nan, tsohon ɗan takarar shugaban ƙasar ya jaddada muhimmancin fara shirye-shirye tun yanzu.

“Duba da abin da ke faruwa a Kano a yau, dole ne mu fara shiri, domin akwai mutanen da suka kuduri aniyar rusa abin da muka gina tsawon lokaci,” in ji shi.

“Manufa ta ita ce yaƙi don kare talakawa a kowane lokaci. Ba zan yi sulhu da masu cin zarafin jama’a ba,” in ji shi.

Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Siyasa

Post navigation

Previous Post: Gwamnatin Kasar Nijar Ta Kame Babban Dan Jarida
Next Post: Shugaban Kasar Ivory Coast Yayi Sauye-Sauye A Majalisar Ministocin Kasar

Karin Labarai Masu Alaka

Tinubu Ya Sayi Fom Din Takarar Shugaban Kasa Afrika
‘Yan Majalisar Wakilai 17 Sun Fice Daga ADC Afrika
Take Hakkin Dan Adam Zai Haifar Da Juyin Juya Hali A Najeriya Najeriya
Shugaban Kasar Brazil: Yakamata Amurka Ta Gurfanar Da Shugaban Venezuela A Kotu Afrika
Gwamnatin Trump Tana Cigaba Da Korar Baki Daga Amurka Afrika
Shugaba Bola Tinubu Ya Saka Hannu A Dokar Zabe Najeriya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Najeriya Da Maroko Sun Kulla Yarjejeniya
  • Pantami Ya Bayyana Dalilin Mayar Da Zaben Sa Abuja
  • Jam’iyar SDP Tana Gudanar Da Babban Taro A Bauchi
  • Rundunar Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Shirya Taron Masu Ruwa Da Tsaki A Jihar Filato
  • Dakaru Sun Hallaka ’Yan Ta’adda Masu Yawa – DHQ

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • ‘Yan Bindiga Sun Jikkata Mutane A Arewacin Kasar Benin Afrika
  • Akwai Doka Mai Tsanani Wajen Mallakar Bindiga A Kasashen Yammacin Turai Labarai
  • Gwamnatin Kano: Zamu Kara Daukar Malamai Domin Inganta Ilimi Najeriya
  • Majalisar Dattawar Najeriya Ta Amince Da Tura Sakamakon Zabe Ta Intanet Labarai
  • Afirka Ta Kudu Tace Bazata Yanke Alaka Da Iran Ba Afrika
  • Fubara Yana Yiwa Dimokraɗiyya Zagon Kasa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Hukumar NAHCON Ta Kamallah Shirye Shiryen Hajjin 2026 A Kasar Saudiya Labarai
  • Amurka Zata Bada Gudumawar Kudi Dala Bilyan 10 Ga Ayyukan Kwamitin Wanzar Da Zaman Lafiyan Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.