Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u Afrika
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa Afrika
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa Afrika
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed Afrika

Kwankwaso Yayi Kakkausar Lafazi Bayan Ficewar Abba Kabir Yusuf Daga NNPP
Published: January 24, 2026 at 5:34 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar NNPP kuma jagoran Kwankwasiyya, Rabiu Musa Kwankwaso, ya sake jaddada tsayuwar sa kan akidun sa na siyasa, yana mai cewa ba zai sayar da ƙa’idojinsa domin amfanin kansa ba.

Kwankwaso ya bayana hakan ne a daidai lokacin da rahotanni ke cewa Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, tare da wasu shugabannin ƙananan hukumomi, wasu ’yan Majalisar Wakilai da wasu mataimaka, sun fice daga jam’iyyar NNPP.

Da yake jawabi ga magoya baya a gidan sa da ke Kano jim kaɗan bayan murabus ɗin gwamnan a ranar Juma’a, Kwankwaso ya ce gwagwarmayar sa ta siyasa tun farko ta ta’allaka ne kan ’yantar da talakawan Najeriya.

“Ni ba na sayarwa ba ne. Akidun siyasar mu ne ke tsayar da ni a kan hanya. Da ace neman riba ta kaina nake yi, da tuni na bi hanya mai sauƙi, kuma da ba ku same ni a nan ba,” in ji shi.

Ya ƙara da cewa ƙungiyar Kwankwasiyya ta tsaya tsayin daka ne bisa ɗabi’u da manufofi na bai ɗaya, ba wai saboda abin duniya ba.

“Manufa da hangen nesan mu ne ke ƙarfafa ni. Da ace kwaɗayi ne ke motsa ni, da tuni na karɓi kuɗi na gudu, kuma da ba ku zo nan nuna goyon baya ba,” ya ƙara da cewa.

Kwankwaso ya kuma buƙaci magoya bayan sa da su fara shiri da wuri gabanin zaɓukan gama-gari na 2027, yana mai gargaɗi kada a yi sakaci.

“Muna buƙatar mutane irin ku da suka sadaukar kuma suka tsaya kan gaskiya. Kada ku yi kasa a gwiwa, domin wata rana za mu cimma burinmu,” in ji shi.

Da yake magana kan abubuwan da ke faruwa a Kano a baya-bayan nan, tsohon ɗan takarar shugaban ƙasar ya jaddada muhimmancin fara shirye-shirye tun yanzu.

“Duba da abin da ke faruwa a Kano a yau, dole ne mu fara shiri, domin akwai mutanen da suka kuduri aniyar rusa abin da muka gina tsawon lokaci,” in ji shi.

“Manufa ta ita ce yaƙi don kare talakawa a kowane lokaci. Ba zan yi sulhu da masu cin zarafin jama’a ba,” in ji shi.

Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Siyasa

Post navigation

Previous Post: Gwamnatin Kasar Nijar Ta Kame Babban Dan Jarida
Next Post: Shugaban Kasar Ivory Coast Yayi Sauye-Sauye A Majalisar Ministocin Kasar

Karin Labarai Masu Alaka

Likitoci Masu Neman Kwarewa Zasu Shiga Yakin Aiki Afrika
Gwamnatin Najeriya Ta Karyata Raɗe-Raɗin Canza Sunan Kasar Da Soke Shari’a A Arewa Afrika
Ana Zargin Tsohon Shugaban Kasar Philippines Da Ta’addaci A Lokacin Mulkinsa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Manchester United: Za Ta Nada Michael Carrick A Matsayin Kocin Riƙon ƙwarya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Magoya Bayan Obi Sun Yi Tutsu Gabanin Zaben 2027 Siyasa
Gwamnatin Sojan Burkina Faso Ta Soke Jam’iyyun Siyasar Kasar Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • PDP Ta Koka Kan Rushe-rushe, Korar Gombawa Motors da Zaɓen Kananan Hukumomi A Gombe Afrika
  • Wani Abu Ya Fashe A Asibitin Bagudo Dake Jihar Kebbi Tsaro
  • Kayan Jinya Da Ayyukan Kiwon Lafiya Suna Barazanar Karewa A Sudan Kiwon Lafiya
  • Shugaban Kasar Madagascar Ya Kori Prime Minista Da ‘Yan Majalisa Afrika
  • Za’ayi Auren Zawarawa Dubu Uku A Kano Afrika
  • Boko Haram Sun Farmaki Sansanin Sojoji A Borno Tsaro
  • Jirgin Ruwan ‘Yan Gudun Hijira Ya Nitse Kogi A Tunisiya Labarai
  • Al’ummar Jihar Nasarawa Suna Cecekuce Bisa Tsaida Aliyu Wadada Takarar Gwamna Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.