Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama Afrika
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara Afrika
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe Afrika
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro Afrika
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa Afrika

Nasarawa Ce Zakara A Wasan Kwallon Kafa Ta Kurame 2025
Published: November 30, 2025 at 7:44 AM | By: Bala Hassan | Updated: November 30, 2025

JIHAR NASARAWA TA ƊAUKI KYAUTAR KWALLON KAFAR KURAME.

Ƙungiyar Kwallon Kafa na Kurame Deaf, ta jihar Nasarawa a Tarayyar Najeriya ta lashe kofin gasar a bana.

Gasar wadda ta ƙunshi jihohi goma, ciki har da Nasarawa, Rivers, Niger, Kaduna, Kano, Kebbi, da masu masaukin baki, Plateau, Adamawa, Bauchi, da FCT, Abuja, ta fara ne a ranar 19 ga Nuwamba, 2025, a cibiyoyi daban-daban a Jos, Jihar Plateau.

Sakatariyar Wasanni ta Musamman na Jihar Nasarawa, Ms Patricia David Oshuwayine, ita ta wakilci Ma’aikatar Matasa da Ci gaban Wasanni ta Jihar Nasarawa a gasar.

Kwamishinan Ci gaban Matasa da Wasanni na Jihar Nasarawa, Hon. Kwanta Yakubu, ya taya Ƙungiyar Ƙwallon Ƙafa ta Kurame na Jihar murna nasarar da suka samu a gasar cin kofin ƙwallon ƙafa ta ƙasa ta karo na 6 da aka gudanar a Jos, Jihar Plateau.

Kwanta ya ce, “Makonni kaɗan da suka gabata, na haɗu da membobin ƙungiyar a sansaninsu da ke Lafia, kafin fara gasar, kuma na ƙarfafa musu gwiwa don su yi duk mai yiwuwa don faranta wa Gwamna Abdullahi Sule da Jihar rai ta hanyar lashe gasar a Jos, kuma zan gabatar da su ga Gwamna.

“A yau, Gwamna Abdullahi Sule da dukkan al’umar Jihar suna alfahari da rawar da ƙungiyar ta taka.

“‘Yan wasanmu masu hazaka sun fafata da manyan ƙungiyoyi daga ko’ina cikin ƙasar, kuma daga ƙarshe sun yi nasara

“Muna yi wa sabbin zakarun ƙasa alƙawarin tarba mai kyau da kuma shirya ya musu liyafa ta musamman a Lafia, Babban Birnin Jiha,” in ji Kwamishinan.

Tawagar ƙungiyar Nasarawa ta samu wannan nasararne bayan da ta doke tawagar ƙungiyar kwallon kafa ta Kurame na Jihar Kaduna da ci 1-0 a ranar Asabar 29 ga watan Nuwamban 2025.

Da yake zantawa da yan jarida mai horas da ƙungiyar na jihar Nasarawa Jafar Umar yace kafin lashe wannan gasar ta wagar Nasarawa ta doke masu ma saukin baki jihar Plateau,Adamawa,Kebbi,da jihar Niger.

Kamar yadda Jami’in hulda da jama’a na Ma’aikatar Matasa da Ci gaban Wasanni na Jihar Nasarawa, Eche Amos ya fitar a wata ta karda da ya rabawa mane ma labarai.

Wasanni

Post navigation

Previous Post: Samar Da Tsaro A Jihar Kano Ba Sai An Sa Siyasa Ba!
Next Post: Sabunta Manhajar Ilimi A Duk Matakai Nasara Ce!

Karin Labarai Masu Alaka

Barcelona na hangen Enrique Ko Arteta Wasanni
Ronaldo Da Messi Ka Iya Hadu A Gasar Cin Kofin Duniya: Ta Ya Ya ? Wasanni
Alkalan Wasannin Kwallon Kafa A Ghana Zasu Samu Inshora Wasanni
Shugaban Hukumar Kwallon Kafa Ta Senegal Yaki Amincewa Da Hukuncin CFA Afrika
Najeriya Ta Kai Wasan Kusa Da Na Karshe A Wasan Dambe Na Matasan Afirka Wasanni
An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Hukumar MDD Tace Wadanda Suka Mutu A Harin Sudan Sun Haura 70 Afrika
  • NYSC – Sai An Gabatar Da Takardar NERD Kafin Shiga Bautar Ƙasa Afrika
  • Shugaba Trump Ya Amince Da Tsawaita Cinikayya Tsakanin Amurka Da Kasashen Afirka Afrika
  • Kudi Sunfi Rayuwar Mutum Muhimmanci A Asibitocin Najeriya Kiwon Lafiya
  • An Gudanar Da Tiyatar Ido Kyauta A Gombe Afrika
  • Shugaban Kasar Ukraine Yace Rasha Tana Bawa Iran Bayanan Sirri Afrika
  • Babban Hafsan Tsaron Najeriya Ya Gargadi Masu Tayar Da Hankali Najeriya
  • Gwamnan Neja Bago Na Cin Zarafin Talakawan Da Suka Zabe Shi Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.