Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Ƙungiyoyin Ƙwadago Sun Ce Albashin ₦70,000 Ya Gaza Biyan Bukatun Ma’aikata Afrika
  • NUJ Gombe Ta Ƙarfafa Bin Ɗa’a A Aikin Jarida, Ta Kaddamar Da Kwamitin Ladabtarwa Afrika
  • Hukumar UBRBDA Ta Fara Raba Kayan Noma A Gombe, Yobe Da Borno Amurka
  • Masu Ruwa Da Tsaki Sun Buƙaci Ƙarin Tallafi Ga Iyaye Mata Masu Shayarwa A Gombe Afrika
  • Rundunar ‘Yan Sandan Gombe Ta Yi Gargaɗi Ga Masu Karya Dokokin Hanya Afrika

Nasarawa Ce Zakara A Wasan Kwallon Kafa Ta Kurame 2025
Published: November 30, 2025 at 7:44 AM | By: Bala Hassan | Updated: November 30, 2025

JIHAR NASARAWA TA ƊAUKI KYAUTAR KWALLON KAFAR KURAME.

Ƙungiyar Kwallon Kafa na Kurame Deaf, ta jihar Nasarawa a Tarayyar Najeriya ta lashe kofin gasar a bana.

Gasar wadda ta ƙunshi jihohi goma, ciki har da Nasarawa, Rivers, Niger, Kaduna, Kano, Kebbi, da masu masaukin baki, Plateau, Adamawa, Bauchi, da FCT, Abuja, ta fara ne a ranar 19 ga Nuwamba, 2025, a cibiyoyi daban-daban a Jos, Jihar Plateau.

Sakatariyar Wasanni ta Musamman na Jihar Nasarawa, Ms Patricia David Oshuwayine, ita ta wakilci Ma’aikatar Matasa da Ci gaban Wasanni ta Jihar Nasarawa a gasar.

Kwamishinan Ci gaban Matasa da Wasanni na Jihar Nasarawa, Hon. Kwanta Yakubu, ya taya Ƙungiyar Ƙwallon Ƙafa ta Kurame na Jihar murna nasarar da suka samu a gasar cin kofin ƙwallon ƙafa ta ƙasa ta karo na 6 da aka gudanar a Jos, Jihar Plateau.

Kwanta ya ce, “Makonni kaɗan da suka gabata, na haɗu da membobin ƙungiyar a sansaninsu da ke Lafia, kafin fara gasar, kuma na ƙarfafa musu gwiwa don su yi duk mai yiwuwa don faranta wa Gwamna Abdullahi Sule da Jihar rai ta hanyar lashe gasar a Jos, kuma zan gabatar da su ga Gwamna.

“A yau, Gwamna Abdullahi Sule da dukkan al’umar Jihar suna alfahari da rawar da ƙungiyar ta taka.

“‘Yan wasanmu masu hazaka sun fafata da manyan ƙungiyoyi daga ko’ina cikin ƙasar, kuma daga ƙarshe sun yi nasara

“Muna yi wa sabbin zakarun ƙasa alƙawarin tarba mai kyau da kuma shirya ya musu liyafa ta musamman a Lafia, Babban Birnin Jiha,” in ji Kwamishinan.

Tawagar ƙungiyar Nasarawa ta samu wannan nasararne bayan da ta doke tawagar ƙungiyar kwallon kafa ta Kurame na Jihar Kaduna da ci 1-0 a ranar Asabar 29 ga watan Nuwamban 2025.

Da yake zantawa da yan jarida mai horas da ƙungiyar na jihar Nasarawa Jafar Umar yace kafin lashe wannan gasar ta wagar Nasarawa ta doke masu ma saukin baki jihar Plateau,Adamawa,Kebbi,da jihar Niger.

Kamar yadda Jami’in hulda da jama’a na Ma’aikatar Matasa da Ci gaban Wasanni na Jihar Nasarawa, Eche Amos ya fitar a wata ta karda da ya rabawa mane ma labarai.

Wasanni

Post navigation

Previous Post: Samar Da Tsaro A Jihar Kano Ba Sai An Sa Siyasa Ba!
Next Post: Sabunta Manhajar Ilimi A Duk Matakai Nasara Ce!

Karin Labarai Masu Alaka

Kungiyar Enyimba: Bamu Da Niyyar Rage Albashin ‘Yan-Wasa Wasanni
An Bude Gasar Bauchi Annual International Polo 2026 Wasanni
FIFA, Ta Raba Jaddawalin Rukuni Na Gasar Kofin Duniya 2026. Wasanni
Senegal Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirka Afcon 2025. Wasanni
Chelle: Rashin Jituwa Tsakanin Osimhen Da Lookman Matsala Ce Ta Cikin Gida Wasanni
Hawan Sallah Daga Masarautar Misau Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Ƙungiyoyin Ƙwadago Sun Ce Albashin ₦70,000 Ya Gaza Biyan Bukatun Ma’aikata
  • NUJ Gombe Ta Ƙarfafa Bin Ɗa’a A Aikin Jarida, Ta Kaddamar Da Kwamitin Ladabtarwa
  • Hukumar UBRBDA Ta Fara Raba Kayan Noma A Gombe, Yobe Da Borno
  • Masu Ruwa Da Tsaki Sun Buƙaci Ƙarin Tallafi Ga Iyaye Mata Masu Shayarwa A Gombe
  • Rundunar ‘Yan Sandan Gombe Ta Yi Gargaɗi Ga Masu Karya Dokokin Hanya

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Kasar Afirka Ta Kudu Ta Tsare Wasu Amurkawa Amurka
  • Dakarun Sojin Najeriya Sun Kashe Yan Kungiyar Lakurawa Afrika
  • Kasar Ghana Ta Bayyana Fataucin Bayi A Matsayin Babban Laifi Afrika
  • Hukumar ICPC Ta Gayyaci Dangote Labarai
  • NITDA Da GOSIDEC Sun Horar Da Ma’aikatan Gombe Don Inganta Ayyukan Gwamnati Afrika
  • An Kafa Majalisar Kotun Sulhu Ta Kano Labarai
  • Musa: “Da Yaddar Allah Zamu Ga Bayan Ta’addanci A Najeriya” Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • GOSEMA Ta Horar Da Mambobin LEMCs A Jihar Gombe Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.