Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Rashin Hanya da Asibiti Ya Jawo Asarar Rayuka A Jihar Gombe – Sarkin Gargajiya Afrika
  • Dakarun Sojin Najeriya Sun Kashe Yan Kungiyar Lakurawa Afrika
  • Shugaba Tinubu Ya Yabawa Dakarun Tsaro Bisa Ceto Matar Marigayi Janar Rabe Afrika
  • Sabuwar Shekarar Musulunci 1448: Kiristoci Sun Yi Murna, Sunyi Kiran Samar Da Hutu Ga Shekarar Musulunci Afrika
  • Sabuwar Shekarar Musulunci: Shugaban Gwamnonin Arewa Ya Yi Kira Da A Yawaita Addu’o’i Da Haɗin Kai Afrika

An Gudanar Da Tiyatar Ido Kyauta A Gombe
Published: May 2, 2026 at 7:35 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

An gudanar da wannan shirin ne ta hannun Hukumar Tara Haraji ta jihar Gombe, ƙarƙashin jagorancin shugabarta, Aisha Adamu, tare da haɗin gwiwar ƙungiyar Imkhahad Development Initiative.

Shirin na tsawon kwanaki uku, wanda aka yi daga ranar ɗaya zuwa uku ga watan Mayu, dubu biyu da ashirin da shida, ya gudana a ƙauyen Hina da ke Ƙaramar Hukumar Yamaltu Deba, inda akayi gwaje-gwaje, shawarwari, magunguna, tiyata da kuma tabarau na gani kyauta ga al’umma.

Da take jawabi a wajen buɗe shirin, Shugabar Hukumar, Aisha Adamu, ta jaddada muhimmancin danganta biyan haraji da ci gaban al’umma kai tsaye. Ta kuma yaba wa Gwamnan jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, bisa goyon bayan da yake bayarwa, wanda ta ce shi ne ya ba da damar aiwatar da irin waɗannan shirye-shirye.

Ta kuma gode wa ƙungiyar Imkhahad Development Initiative, musamman shugabarta, Umulkairi Adamu, bisa jajircewarta wajen ayyukan jin ƙai da haɗin gwiwa domin magance matsalolin lafiyar idanu a yankunan da ba su da isasshen kulawa.

Shugabannin al’umma ma sun yaba da wannan shiri. Sarkin Yamaltu, Abubakar Aliyu, wanda Alhaji Isa Idris Tela, Hakimin Hina ya wakilta, ya bayyana shirin a matsayin mai muhimmanci kuma mai kawo sauyi, yana mai cewa ingantacciyar lafiyar idanu za ta ƙara yawan aiki da inganta rayuwar al’umma.

A nasa bangaren, Likitan da ya jagoranci shirin daga asibitin Shifa Eye Care, Dokta Lawali Mohammed Kumo, ya shawarci waɗanda suka amfana da su bi umarnin likitoci da kula da kansu bayan tiyata domin samun cikakken waraka.

Abin lura a yayin shirin shi ne, wasu daga cikin waɗanda suka zo ba sa gani sun koma gidajensu suna gani bayan an yi musu tiyata.

Masu amfana da shirin sun bayyana godiyarsu, suna mai cewa wannan taimako ya dawo musu da gani tare da ba su damar ci gaba da gudanar da ayyukansu na yau da kullum.

Shugabar Hukumar Tara Haraji ta Jihar Gombe ta ce shirin na ci gaba da zama hujja cewa yadda ake tara haraji yadda ya kamata na iya haifar da ayyukan ci gaba masu amfani, tare da ƙarfafa amincewar jama’a da kuma ƙara yawan biyan haraji da son rai.

Afrika, Kiwon Lafiya, Labarai, Najeriya

Post navigation

Previous Post: Shugaba Tinubu Ya Tafi Kasar Faransa
Next Post: Tsohon Ma’aikacin VOA Saleh Shehu Ashaka Ya Rasu

Karin Labarai Masu Alaka

Jamhuriyar Congo Zata Cigaba Da Fitar Da Ma’adanai Afrika
China Ta Yi Kira Da Kasashen Gabas Ta Tsakiya Su Hada Kai Labarai
Jiragen Ruwa Suna Biyayya Ga Dokar Hana Ketare Ruwa Amurka
Shugaban Kasar Afirka Ta Tsakiya Ya Roki Rasha Ta Taimakawa Kasar Afrika
Akwai Bukatar Bin Dokokin Tuki A Kan Hanyoyi Labarai
An Gudanar Da Zanga-Zanga A Guinea-Bissau Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Rashin Hanya da Asibiti Ya Jawo Asarar Rayuka A Jihar Gombe – Sarkin Gargajiya
  • Dakarun Sojin Najeriya Sun Kashe Yan Kungiyar Lakurawa
  • Shugaba Tinubu Ya Yabawa Dakarun Tsaro Bisa Ceto Matar Marigayi Janar Rabe
  • Sabuwar Shekarar Musulunci 1448: Kiristoci Sun Yi Murna, Sunyi Kiran Samar Da Hutu Ga Shekarar Musulunci
  • Sabuwar Shekarar Musulunci: Shugaban Gwamnonin Arewa Ya Yi Kira Da A Yawaita Addu’o’i Da Haɗin Kai

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Sakataren Harkokin Wajen Amurka Yace Rahoton Kasashe Biyar Akan Rasha Yana Dauke Da Damuwa Amurka
  • Salmanu: Ci Gaban Wikki Tourist FC Shine A Gaba Na Wasanni
  • Eziekel Gomos Ya Zamo Babban Daraktan Sakatariyar Zauren Gwamnonin Arewa Najeriya
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai Afrika
  • Domin Karfafa Tsaro Babban Hafsan Sojin Najeriya Ya Ziyarci Jos Afrika
  • Najeriya, Sojoji Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Sama Da 80, Sun Ceto 34 Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Kudi Sunfi Rayuwar Mutum Muhimmanci A Asibitocin Najeriya Kiwon Lafiya
  • Shugaban Amurka Yace Zayyi Wahala A Cimma Yarjejeniya Tsakanin Isra’ila, Amurka Da Iran Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.