Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Mohammed Abdullahi Abubakar Ya Sayi fom Don Tsayawa Takarar kujeran Gwamnan Bauchi A APC 2027 Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Shugaba Tinubu Ya Bukaci Samar Da Zaman Lafiya A Filato Afrika
  • Kotu Tayi Watsi Da Tarukan ADC Bangaren David Mark Afrika
  • NAHCON Ta Fitar Da Jadawalin Hajjin Bana 2027 Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Ta Jinjinawa Saudiya Afrika

An Gudanar Da Tiyatar Ido Kyauta A Gombe
Published: May 2, 2026 at 7:35 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

An gudanar da wannan shirin ne ta hannun Hukumar Tara Haraji ta jihar Gombe, ƙarƙashin jagorancin shugabarta, Aisha Adamu, tare da haɗin gwiwar ƙungiyar Imkhahad Development Initiative.

Shirin na tsawon kwanaki uku, wanda aka yi daga ranar ɗaya zuwa uku ga watan Mayu, dubu biyu da ashirin da shida, ya gudana a ƙauyen Hina da ke Ƙaramar Hukumar Yamaltu Deba, inda akayi gwaje-gwaje, shawarwari, magunguna, tiyata da kuma tabarau na gani kyauta ga al’umma.

Da take jawabi a wajen buɗe shirin, Shugabar Hukumar, Aisha Adamu, ta jaddada muhimmancin danganta biyan haraji da ci gaban al’umma kai tsaye. Ta kuma yaba wa Gwamnan jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, bisa goyon bayan da yake bayarwa, wanda ta ce shi ne ya ba da damar aiwatar da irin waɗannan shirye-shirye.

Ta kuma gode wa ƙungiyar Imkhahad Development Initiative, musamman shugabarta, Umulkairi Adamu, bisa jajircewarta wajen ayyukan jin ƙai da haɗin gwiwa domin magance matsalolin lafiyar idanu a yankunan da ba su da isasshen kulawa.

Shugabannin al’umma ma sun yaba da wannan shiri. Sarkin Yamaltu, Abubakar Aliyu, wanda Alhaji Isa Idris Tela, Hakimin Hina ya wakilta, ya bayyana shirin a matsayin mai muhimmanci kuma mai kawo sauyi, yana mai cewa ingantacciyar lafiyar idanu za ta ƙara yawan aiki da inganta rayuwar al’umma.

A nasa bangaren, Likitan da ya jagoranci shirin daga asibitin Shifa Eye Care, Dokta Lawali Mohammed Kumo, ya shawarci waɗanda suka amfana da su bi umarnin likitoci da kula da kansu bayan tiyata domin samun cikakken waraka.

Abin lura a yayin shirin shi ne, wasu daga cikin waɗanda suka zo ba sa gani sun koma gidajensu suna gani bayan an yi musu tiyata.

Masu amfana da shirin sun bayyana godiyarsu, suna mai cewa wannan taimako ya dawo musu da gani tare da ba su damar ci gaba da gudanar da ayyukansu na yau da kullum.

Shugabar Hukumar Tara Haraji ta Jihar Gombe ta ce shirin na ci gaba da zama hujja cewa yadda ake tara haraji yadda ya kamata na iya haifar da ayyukan ci gaba masu amfani, tare da ƙarfafa amincewar jama’a da kuma ƙara yawan biyan haraji da son rai.

Afrika, Kiwon Lafiya, Labarai, Najeriya

Post navigation

Previous Post: Shugaba Tinubu Ya Tafi Kasar Faransa

Karin Labarai Masu Alaka

Wata Kotu A Abuja Ta Wanke Abba Kyari Afrika
NLC Ta Yabawa Gwamnan Gombe Inuwa Yahaya Najeriya
Akwai Yiwuwar Iran Da Amurka Su Cimma Matsayar Dakatar Da Shirin Nukiliya Amurka
Gwamnatin Tarayya Tana Neman Kudi Domin Aiwatar Da Kasafin Kudin 2026 Najeriya
Shugaba Donald Trump Ya Bayyana Cewa Yana Cikin Masu Zaben Sabon Jagoran Iran Amurka
Rasha Takai Hari Ukraine Da Jirgi Marar Matuki Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • An Gudanar Da Tiyatar Ido Kyauta A Gombe
  • Shugaba Tinubu Ya Tafi Kasar Faransa
  • Gwamna Bala Kauran Bauchi Ya Koma Jam’iyar APM
  • Sojin Saman Najeriya Sun Lalata Sansanonin ‘Yan Ta’adda
  • ‘Yan Sanda A Jihar Gombe Sun Karyata Kona Gidan Nafiu Bala

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Gwamnatin Kano Ta Samar Da Wasu Dabarun Inganta Tsaro Tsaro
  • Gwamnatin Tarayya Tana Neman Kudi Domin Aiwatar Da Kasafin Kudin 2026 Najeriya
  • Jami’an Tsaron Pakistan Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Labarai
  • An Gudanar da Taron Kwana Biyu kan Tsarin Sa Ido da Tantance Ayyukan AGILE a Jihar Gombe  Afrika
  • Sojojin Amurka Sun Isa Najeriya Don Yaki Da Ta’addanci Amurka
  • Kungiyar ‘Yan Jarida Ta Najeriya Ta Tabbatar Da Kyautata Rayuwar Mambobin ta Labarai
  • Ruwan Sama Ya Dai-Daita ‘Yan Gudun Hijira A Gaza Labarai
  • Jamhuriyar Nijar Ta Fitar Da Doka Domin Kare ‘Yancin ‘Yan Kasar Tsaro
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.