Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Mohammed Abdullahi Abubakar Ya Sayi fom Don Tsayawa Takarar kujeran Gwamnan Bauchi A APC 2027 Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Shugaba Tinubu Ya Bukaci Samar Da Zaman Lafiya A Filato Afrika
  • Kotu Tayi Watsi Da Tarukan ADC Bangaren David Mark Afrika
  • NAHCON Ta Fitar Da Jadawalin Hajjin Bana 2027 Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Ta Jinjinawa Saudiya Afrika

Shugaba Tinubu Ya Tafi Kasar Faransa
Published: May 2, 2026 at 4:36 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu zai tashi daga Abuja a ranar Asabar, 2 ga Mayu, 2026, domin gudanar da ziyarar diflomasiyya zuwa ƙasashe uku wato France, Kenya da Rwanda, a wani yunƙuri na ƙarfafa hulɗar Najeriya da ƙasashen duniya da kuma bunƙasa gyaran tattalin arziki.

A cewar wata sanarwa da Mai Bai wa Shugaban Ƙasa Shawara na Musamman kan Yaɗa Labarai da Tsare-tsare, Bayo Onanuga, ya fitar a ranar Juma’a, jadawalin tafiyar shugaban zai fara ne da ziyara zuwa France kafin daga bisani ya wuce Nairobi a ƙasar Kenya, inda zai halarci taron Africa-France Summit da zai fara a mako mai zuwa.

Ana sa ran taron, wanda Shugaban Faransa Emmanuel Macron da Shugaban Kenya William Ruto za su jagoranta tare, zai mayar da hankali kan muhimman batutuwa na duniya da nahiyar Afirka, ciki har da sauyin makamashi, bunƙasa masana’antu masu kare muhalli, sauyin fasahar zamani, matakan yaƙi da sauyin yanayi, da sake fasalin tsarin kuɗaɗen duniya.

Bayo Onanuga ya ce halartar Shugaba Bola Ahmed Tinubu a taron da za a yi daga 11 zuwa 12 ga Mayu, zai nuna cikakken ƙudirin Najeriya na ƙarfafa alaƙar dabaru da ƙasashen Afirka da kuma Jamhuriyar Faransa.

Taken taron shi ne, “Africa Forward: Africa-France Partnerships for Innovation and Growth,” kuma zai zama babban dandali da shugabannin Afirka da na Faransa za su tattauna kan muhimman batutuwa kamar sauya tattalin arziki, jurewa matsalolin sauyin yanayi, bunƙasa ababen more rayuwa, ƙarfafa matasa, ci gaban fasaha, da kuma gina zaman lafiya.

Sanarwar ta ce, “A wajen taron, Shugaba Bola Ahmed Tinubu zai gabatar da jawabi da zai bayyana gyare-gyaren da gwamnatin sa ke yi domin mayar da Najeriya wuri mafi dacewa ga zuba jari da ci gaba.”

Afrika, Labarai, Najeriya

Post navigation

Previous Post: Gwamna Bala Kauran Bauchi Ya Koma Jam’iyar APM

Karin Labarai Masu Alaka

Kotu A Kasar Tunisiya Ta Daure Wani Babban Dan Kasuwa Da Wasu ‘Yan Majalisa Afrika
Kasashen Thailand Da Cambodia Sun Amince Da Tsagaita Wuta Labarai
An Saka Dokar Hana Fita A Jos Ta Arewa Afrika
APC Ta Yi Babban Taron Amincewa Da Shugabannin Jam’iyyar Ba Hamayya Najeriya
Kakakin Majalisar Kasar Amurka Yana Tsaka Mai Wuya Game Da Kasafin Kudi Amurka
An Garkame Dan Majalisa Watannin Takwas A Kasar Tunisiya Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Shugaba Tinubu Ya Tafi Kasar Faransa
  • Gwamna Bala Kauran Bauchi Ya Koma Jam’iyar APM
  • Sojin Saman Najeriya Sun Lalata Sansanonin ‘Yan Ta’adda
  • ‘Yan Sanda A Jihar Gombe Sun Karyata Kona Gidan Nafiu Bala
  • Mohammed Abdullahi Abubakar Ya Sayi fom Don Tsayawa Takarar kujeran Gwamnan Bauchi A APC 2027

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Amurka Zata Fice Daga Iran Cikin Gaggawa Afrika
  • Gwamnatin Tarayya Tana Neman Kudi Domin Aiwatar Da Kasafin Kudin 2026 Najeriya
  • Afirka Ta Kudu Tace Bazata Yanke Alaka Da Iran Ba Afrika
  • Tinubu: Munsayi Jiragen Yaki Daga Wajen Amurka Amurka
  • Gwamnatin Tarayya Tayi Baje Kolin Nasarorin Tinubu Afrika
  • Hotunan Hawan Sallah A Masarautar Bauchi Afrika
  • Majalisar Dattawar Najeriya Ta Amince Da Tura Sakamakon Zabe Ta Intanet Labarai
  • Iran Ta Tsagaita Kai Hare Hare Makwabta Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.