Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu zai tashi daga Abuja a ranar Asabar, 2 ga Mayu, 2026, domin gudanar da ziyarar diflomasiyya zuwa ƙasashe uku wato France, Kenya da Rwanda, a wani yunƙuri na ƙarfafa hulɗar Najeriya da ƙasashen duniya da kuma bunƙasa gyaran tattalin arziki.
A cewar wata sanarwa da Mai Bai wa Shugaban Ƙasa Shawara na Musamman kan Yaɗa Labarai da Tsare-tsare, Bayo Onanuga, ya fitar a ranar Juma’a, jadawalin tafiyar shugaban zai fara ne da ziyara zuwa France kafin daga bisani ya wuce Nairobi a ƙasar Kenya, inda zai halarci taron Africa-France Summit da zai fara a mako mai zuwa.
Ana sa ran taron, wanda Shugaban Faransa Emmanuel Macron da Shugaban Kenya William Ruto za su jagoranta tare, zai mayar da hankali kan muhimman batutuwa na duniya da nahiyar Afirka, ciki har da sauyin makamashi, bunƙasa masana’antu masu kare muhalli, sauyin fasahar zamani, matakan yaƙi da sauyin yanayi, da sake fasalin tsarin kuɗaɗen duniya.
Bayo Onanuga ya ce halartar Shugaba Bola Ahmed Tinubu a taron da za a yi daga 11 zuwa 12 ga Mayu, zai nuna cikakken ƙudirin Najeriya na ƙarfafa alaƙar dabaru da ƙasashen Afirka da kuma Jamhuriyar Faransa.
Taken taron shi ne, “Africa Forward: Africa-France Partnerships for Innovation and Growth,” kuma zai zama babban dandali da shugabannin Afirka da na Faransa za su tattauna kan muhimman batutuwa kamar sauya tattalin arziki, jurewa matsalolin sauyin yanayi, bunƙasa ababen more rayuwa, ƙarfafa matasa, ci gaban fasaha, da kuma gina zaman lafiya.
Sanarwar ta ce, “A wajen taron, Shugaba Bola Ahmed Tinubu zai gabatar da jawabi da zai bayyana gyare-gyaren da gwamnatin sa ke yi domin mayar da Najeriya wuri mafi dacewa ga zuba jari da ci gaba.”


