Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Rashin Hanya da Asibiti Ya Jawo Asarar Rayuka A Jihar Gombe – Sarkin Gargajiya Afrika
  • Dakarun Sojin Najeriya Sun Kashe Yan Kungiyar Lakurawa Afrika
  • Shugaba Tinubu Ya Yabawa Dakarun Tsaro Bisa Ceto Matar Marigayi Janar Rabe Afrika
  • Sabuwar Shekarar Musulunci 1448: Kiristoci Sun Yi Murna, Sunyi Kiran Samar Da Hutu Ga Shekarar Musulunci Afrika
  • Sabuwar Shekarar Musulunci: Shugaban Gwamnonin Arewa Ya Yi Kira Da A Yawaita Addu’o’i Da Haɗin Kai Afrika

Shugaba Tinubu Ya Tafi Kasar Faransa
Published: May 2, 2026 at 4:36 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu zai tashi daga Abuja a ranar Asabar, 2 ga Mayu, 2026, domin gudanar da ziyarar diflomasiyya zuwa ƙasashe uku wato France, Kenya da Rwanda, a wani yunƙuri na ƙarfafa hulɗar Najeriya da ƙasashen duniya da kuma bunƙasa gyaran tattalin arziki.

A cewar wata sanarwa da Mai Bai wa Shugaban Ƙasa Shawara na Musamman kan Yaɗa Labarai da Tsare-tsare, Bayo Onanuga, ya fitar a ranar Juma’a, jadawalin tafiyar shugaban zai fara ne da ziyara zuwa France kafin daga bisani ya wuce Nairobi a ƙasar Kenya, inda zai halarci taron Africa-France Summit da zai fara a mako mai zuwa.

Ana sa ran taron, wanda Shugaban Faransa Emmanuel Macron da Shugaban Kenya William Ruto za su jagoranta tare, zai mayar da hankali kan muhimman batutuwa na duniya da nahiyar Afirka, ciki har da sauyin makamashi, bunƙasa masana’antu masu kare muhalli, sauyin fasahar zamani, matakan yaƙi da sauyin yanayi, da sake fasalin tsarin kuɗaɗen duniya.

Bayo Onanuga ya ce halartar Shugaba Bola Ahmed Tinubu a taron da za a yi daga 11 zuwa 12 ga Mayu, zai nuna cikakken ƙudirin Najeriya na ƙarfafa alaƙar dabaru da ƙasashen Afirka da kuma Jamhuriyar Faransa.

Taken taron shi ne, “Africa Forward: Africa-France Partnerships for Innovation and Growth,” kuma zai zama babban dandali da shugabannin Afirka da na Faransa za su tattauna kan muhimman batutuwa kamar sauya tattalin arziki, jurewa matsalolin sauyin yanayi, bunƙasa ababen more rayuwa, ƙarfafa matasa, ci gaban fasaha, da kuma gina zaman lafiya.

Sanarwar ta ce, “A wajen taron, Shugaba Bola Ahmed Tinubu zai gabatar da jawabi da zai bayyana gyare-gyaren da gwamnatin sa ke yi domin mayar da Najeriya wuri mafi dacewa ga zuba jari da ci gaba.”

Afrika, Labarai, Najeriya

Post navigation

Previous Post: Gwamna Bala Kauran Bauchi Ya Koma Jam’iyar APM
Next Post: An Gudanar Da Tiyatar Ido Kyauta A Gombe

Karin Labarai Masu Alaka

Kungiyar Kwallon Mata Sun Tsallaka Iyakar Turkiyya Zuwa Iran Afrika
Farashin Mai Ya Cigaba Da Tashi Afrika
Shugaban Majalisar Tarayyar Turai Yace Rasha Tana Cin Ribar Yakin Gabas Ta Tsakiya Afrika
Jirgin Sojin Saman Najeriya Yayi Hatsari a Jihar Neja Labarai
An Maka Wasu Jami’an Immigration A Kotu Bisa Zargin Rashin Da’a A Birtaniya Labarai
Najeriya Da Poland Za Su Hada Kai Kan Tsaro da Bunƙasa Tattalin Arziki Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Rashin Hanya da Asibiti Ya Jawo Asarar Rayuka A Jihar Gombe – Sarkin Gargajiya
  • Dakarun Sojin Najeriya Sun Kashe Yan Kungiyar Lakurawa
  • Shugaba Tinubu Ya Yabawa Dakarun Tsaro Bisa Ceto Matar Marigayi Janar Rabe
  • Sabuwar Shekarar Musulunci 1448: Kiristoci Sun Yi Murna, Sunyi Kiran Samar Da Hutu Ga Shekarar Musulunci
  • Sabuwar Shekarar Musulunci: Shugaban Gwamnonin Arewa Ya Yi Kira Da A Yawaita Addu’o’i Da Haɗin Kai

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Jam’iyyar APC Ta Rantsar Da Sabbin Shugabanni a Jihar Neja Labarai
  • Gwamnatin Kasar Guinea Ta Soke Wasu Jam’iyyun Siyasa Afrika
  • Tattalin Arzikin Kasar Botswana Zai Farfado Afrika
  • Atiku Ya Zargi Gwamnati Da Kama ‘Yan Adawa Labarai
  • Babban Bankin Najeriya Ya Rage Kudin Ruwa Da Kashi Daya Cikin Dari Labarai
  • Kasashe Biyar Zasu Tura Sojoji Domin Ayyukan Wanzar Da Zaman Lafiya A Gaza Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Kimanin Mutane 200 Ne Suka A Mutu A Wani Harin Jirgin Yakin Sojin Najeriya Afrika
  • Farashin Mai Yana Cigaba Da Karuwa Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.