Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Rundunar ‘Yan Sandan Gombe Ta Kuɓutar da Yaro Daga Hannun Masu Garkuwa Afrika
  • Tinubu Ya Buɗe Katafaren Kamfanin Sarrafa Lithium Domin Bunƙasa Tattalin Arziki Afrika
  • Sojoji Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 1,597, Sun Ceto Mutane 1,516 – DHQ Afrika
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u Afrika
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa Afrika

Atiku Ya Zargi Gwamnati Da Kama ‘Yan Adawa
Published: December 12, 2025 at 11:05 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Tsohon Mataimakin Shugaban Kasar Najeriya, Atiku Abubakar, ya zargi EFCC da kauce wa ka’idar aikin ta na yaki da cin hanci, yana mai cewa hukumar ta koma “makamin siyasa” da ke farautar ’yan adawa.

A wata sanarwa da ofishinsa ya fitar a Abuja, Atiku ya ce Siyasantar da binciken cin hanci ya lahanta kimar EFCC, yana mai zargin hukumar da zaben wadanda za ta bincika bisa siyasa, ba bisa hujjoji ba.

Ya ce kama tsohon Babban Lauyan Gwamnatin tarayya, Abubakar Malami (SAN), wani bangare ne na bin ’yan adawa cikin son zuciya, yana tuhumar EFCC da zama “reshen APC” da ke kokarin kafa tsarin jam’iyya ɗaya.

Atiku ya nuna cewa EFCC ta tsananta aiki ne bayan jam’iyyar ADC ta karu a matsayin babbar Jam’iyyar adawa, inda ya ambaci matakan da ya ce an dauka kan Malami da tsohon gwamnan Sokoto, Aminu Waziri Tambuwal, yayin da ake watsi da zarge-zargen da suka shafi magoya bayan gwamnati.

Ya kuma zargi gwamnatin Shugaba Bola Tinubu da bai wa wasu tsoffin gwamnoni da ke da shari’o’in cin hanci mukaman gwamnati, yana cewa EFCC ta kasa nuna rashin amincewa.

Atiku ya yi ikirarin cewa da Malami ya koma APC, “da ba za a taba taba shi ba,” yana mai zargin hukumar da amfani da tsoratarwa don tilasta ’yan siyasa shiga jam’iyyar gwamnati.

Ya yi gargadi cewa ba za a samu ingantaccen yaki da cin hanci ba idan aka ci gaba da siyasantar da hukumomi, yana kira ga EFCC ta cire kanta daga tasirin siyasa domin kare mutuncin ta.

Labarai

Post navigation

Previous Post: Rashin Tsaro: Gwamnati Ta Bada Umarnin Daukar Ma’aikata Sama Da 94,000
Next Post: Ministan Tsaro Ya Umarci Janye Sojoji Daga Shingayen Bincike A Tituna

Karin Labarai Masu Alaka

‘Yan Sanda Sun Kama Mutane 33 Bisa Zargin Kai Hari A Jihar Kwara Afrika
Gwamnan Jihar Kebbi Ya Amince Da Kasafin Kudi Mai Sauya Fasali Da Karfafa Rayuwar Al’umma Labarai
‘Yan Bindiga Sun Jikkata Mutane A Arewacin Kasar Benin Afrika
Kasar Botswana Na Samun Kudaden Shiga Da Lu’ulu’u Labarai
Hukumomi A Kasar Syri Lanka Suna Kokarin Fidda Jirgin Yakin Iran Daga Kasar Afrika
Hukumar Upper Benue Zata Inganta Noma A Dadinkowa Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Rundunar ‘Yan Sandan Gombe Ta Kuɓutar da Yaro Daga Hannun Masu Garkuwa
  • Tinubu Ya Buɗe Katafaren Kamfanin Sarrafa Lithium Domin Bunƙasa Tattalin Arziki
  • Sojoji Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 1,597, Sun Ceto Mutane 1,516 – DHQ
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • An Kai Shugaban Kasar Venezuela Kotu Amurka
  • Ranar Talata Amurka Da Isra’ila Sun Cigaban Da Kai Farmaki Iran Afrika
  • Harin Bom Din Maiduguri Ya Kashe Mutane Biyar Ya Raunata Fiye Da Talatin Najeriya
  • Gwamnatin Kano Ta Kafa Kwamitin Dawo Da Kudaden Ma’aikata Afrika
  • Sakamakon Rikicin Gabas Ta Tsakiya Farashin Mai Ya Karu Labarai
  • Majalisar Tattalin Arzikin Najeriya Ta Bawa Gwamnan Kebbi Mukamin Kyautata Harkar Kiwo Najeriya
  • Prime Ministar Italiya Ta Ziyarci Saudi Arabia Afrika
  • Amurka Ta Kama Tsohon Ministan Kudin Kasar Ghana Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.