Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Atiku Ya Zargi Gwamnati Da Kama ‘Yan Adawa
Published: December 12, 2025 at 11:05 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Tsohon Mataimakin Shugaban Kasar Najeriya, Atiku Abubakar, ya zargi EFCC da kauce wa ka’idar aikin ta na yaki da cin hanci, yana mai cewa hukumar ta koma “makamin siyasa” da ke farautar ’yan adawa.

A wata sanarwa da ofishinsa ya fitar a Abuja, Atiku ya ce Siyasantar da binciken cin hanci ya lahanta kimar EFCC, yana mai zargin hukumar da zaben wadanda za ta bincika bisa siyasa, ba bisa hujjoji ba.

Ya ce kama tsohon Babban Lauyan Gwamnatin tarayya, Abubakar Malami (SAN), wani bangare ne na bin ’yan adawa cikin son zuciya, yana tuhumar EFCC da zama “reshen APC” da ke kokarin kafa tsarin jam’iyya ɗaya.

Atiku ya nuna cewa EFCC ta tsananta aiki ne bayan jam’iyyar ADC ta karu a matsayin babbar Jam’iyyar adawa, inda ya ambaci matakan da ya ce an dauka kan Malami da tsohon gwamnan Sokoto, Aminu Waziri Tambuwal, yayin da ake watsi da zarge-zargen da suka shafi magoya bayan gwamnati.

Ya kuma zargi gwamnatin Shugaba Bola Tinubu da bai wa wasu tsoffin gwamnoni da ke da shari’o’in cin hanci mukaman gwamnati, yana cewa EFCC ta kasa nuna rashin amincewa.

Atiku ya yi ikirarin cewa da Malami ya koma APC, “da ba za a taba taba shi ba,” yana mai zargin hukumar da amfani da tsoratarwa don tilasta ’yan siyasa shiga jam’iyyar gwamnati.

Ya yi gargadi cewa ba za a samu ingantaccen yaki da cin hanci ba idan aka ci gaba da siyasantar da hukumomi, yana kira ga EFCC ta cire kanta daga tasirin siyasa domin kare mutuncin ta.

Labarai

Post navigation

Previous Post: Rashin Tsaro: Gwamnati Ta Bada Umarnin Daukar Ma’aikata Sama Da 94,000
Next Post: Ministan Tsaro Ya Umarci Janye Sojoji Daga Shingayen Bincike A Tituna

Karin Labarai Masu Alaka

Rahoton Leken Asiri Yanuna Cewa Harin Amurka Bazai Samar Da Shugabanci A Iran Ba Afrika
Amurka Da Tarayyar Turai Sun Fidda Sanarwa Afrika
Tattaunawar Nukiliya Tsakanin Iran Da Amurka Yana Tasirin Akan Farashin Albarkatun Mai Amurka
Harin Iran A Kasar Saudiya Ya Haifar Da Tattaunawa Tsakanin Shugabanni Afrika
Gwamnatin Tinubu Zata Gyara Hanyar Akwanga Zuwa Jos Labarai
Wata Kotu A Abuja Ta Wanke Abba Kyari Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Yakin Gabas Ta Tsakiya Ya Kawo Cikas Ga Cinikin Nama A Kenya
  • Sabon Jagoran Addinin Iran Mojtaba Khameni Yaji Rauni Kuma Ya Nakasa
  • Shugaba Trump Yace Amurka Takai Hari Kharg Tsibiri a Kasar Iran
  • MDD: Fiye Da Farar Hula Metan 200 Suka Mutu A Sudan
  • Jami’ai A Afirka Sunce Tashin Farashin Mai Kalubale Ne Ga Tattalin Arziki

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Gwamnatin Afirka Ta Kudu Na Kokarin Kafa Wasu Dokoki A Kasar Labarai
  • An Damke Wani Likita Da Ke Taimakawa ‘Yan-Ta’adda Najeriya
  • Ghana Tayi Watsi Da Yarjejeniya Akan Hakar Ma’adanai Afrika
  • Amurka Ta Kai Hari Kan ‘Yan ISISI A Jihar Sakkwato Bisa Rokon Gwamnatin Najeriya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • “Banga Abun Da Zai Canza Ba A Nadin Janar Christopher Ministan Tsaro” Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Somaliya Da MDD Sun Bayyana Cewa Kimanin Mutane Miliyan Shida Da Rabi Suna Fuskantar Barazanar Yunwa Labarai
  • Kasar Kenya Zata Samar Da Makamashi Labarai
  • Kasar Gambiya Ta Gayawa Kotun MDD Shirin Myanmar Akan Musulmai Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.