Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

Atiku Ya Zargi Gwamnati Da Kama ‘Yan Adawa
Published: December 12, 2025 at 11:05 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Tsohon Mataimakin Shugaban Kasar Najeriya, Atiku Abubakar, ya zargi EFCC da kauce wa ka’idar aikin ta na yaki da cin hanci, yana mai cewa hukumar ta koma “makamin siyasa” da ke farautar ’yan adawa.

A wata sanarwa da ofishinsa ya fitar a Abuja, Atiku ya ce Siyasantar da binciken cin hanci ya lahanta kimar EFCC, yana mai zargin hukumar da zaben wadanda za ta bincika bisa siyasa, ba bisa hujjoji ba.

Ya ce kama tsohon Babban Lauyan Gwamnatin tarayya, Abubakar Malami (SAN), wani bangare ne na bin ’yan adawa cikin son zuciya, yana tuhumar EFCC da zama “reshen APC” da ke kokarin kafa tsarin jam’iyya ɗaya.

Atiku ya nuna cewa EFCC ta tsananta aiki ne bayan jam’iyyar ADC ta karu a matsayin babbar Jam’iyyar adawa, inda ya ambaci matakan da ya ce an dauka kan Malami da tsohon gwamnan Sokoto, Aminu Waziri Tambuwal, yayin da ake watsi da zarge-zargen da suka shafi magoya bayan gwamnati.

Ya kuma zargi gwamnatin Shugaba Bola Tinubu da bai wa wasu tsoffin gwamnoni da ke da shari’o’in cin hanci mukaman gwamnati, yana cewa EFCC ta kasa nuna rashin amincewa.

Atiku ya yi ikirarin cewa da Malami ya koma APC, “da ba za a taba taba shi ba,” yana mai zargin hukumar da amfani da tsoratarwa don tilasta ’yan siyasa shiga jam’iyyar gwamnati.

Ya yi gargadi cewa ba za a samu ingantaccen yaki da cin hanci ba idan aka ci gaba da siyasantar da hukumomi, yana kira ga EFCC ta cire kanta daga tasirin siyasa domin kare mutuncin ta.

Labarai

Post navigation

Previous Post: Rashin Tsaro: Gwamnati Ta Bada Umarnin Daukar Ma’aikata Sama Da 94,000
Next Post: Ministan Tsaro Ya Umarci Janye Sojoji Daga Shingayen Bincike A Tituna

Karin Labarai Masu Alaka

Yohanna YD Buru: Makon Haɗin Kan Addinai Ya Ƙarfafa Ilimin Zaman Lafiya A Najeriya Labarai
Shugaban Libya Ya Sayi Jirage Marasa Matuka Afrika
Amurka Zata Tantance Fararen Fata ‘Yan Afirka Ta Kudu Afrika
Kungiyoyin Fararen Hula A Gombe Sun Bukaci A Bawa Mata Jagoranci Afrika
Gabannin Harin Amurka Da Isra’ila Iran Farisa Ta Shirya Nata Afrika
Kannywood: Ali Nuhu Ya Shiga Kwamitin Yaƙin Neman Zaɓen Tinubu Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Amurka Zata Fice Daga Iran Cikin Gaggawa Afrika
  • Musa: “Da Yaddar Allah Zamu Ga Bayan Ta’addanci A Najeriya” Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Sojoji Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 1,597, Sun Ceto Mutane 1,516 – DHQ Afrika
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan-Bindiga Sun Yi Awon Gaba Da Daliban St. Mary! Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Shugaban Mulkin Soja A Mali Ya Kirkiro Mukami Kamar Minista Afrika
  • Tinubu Ya Nada Shugabannin Hukumar NERC Najeriya
  • Hukumar ‘Yan Sanda Ta Dawo Da Dokar Zirga Zirgar Babura A Jihar Gombe Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.