A Najeriya ‘yan sandan kasar sun kama mutane 33 wadanda ta bayyana su a zaman ‘yan banga kan zargin wani hari da aka kai kan wani coci a jahar kwara cikin watan Nuwamba, har aka yi garkuwa da mutane 38, kamar yadda rundunar ta fada a ranar talata, a zaman wani mataki na murkushe masu tada husuma a kasa.
Kakakin rundunar ‘Yan sandan kasar Anthony Okon, yace gungun bata garin ne suka kai harin na ranar 18 ga watan Nuwamba kan cocin Christ Apostilic Chuch dake garin da ake kira Eruku, haka rundundar tana zargin mutanen da laifin wasu sace sacen mutane, da dabbobi, da kuma fashi da makami a fadin yankin.
Sanarwar da kakakin rundunar ‘Yan sandan ya bayar, tace an kama mutanen ne a wasu somame da suka kai fadin jihar Kwara da makwabciyarta jahar kogi, bayan da suka sami bayanan sirri daga mutum da na’urori, azaman wani bangare na matakan tsaro da ya kai ga kama mutane 50 wadanda ake tuhuma, tun cikin watan Janairun bana.
Najeriya ta juma tana fama da matsalolin tsaro, da suka hada da sace sacen gungun mutane, domin neman kudin fansa, da fitinar ‘yan bindiga da wasu mayakan sakai.


